Connect with us

Hangen Dala

Najeriya ce kan gaba wajen fama da talauci – MDD

Published

on

Wani Rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana Najeriya a matsayin kasa da ta yi zarra a yawan matalauta a nahiyar Afirka, da mutum akalla miliyan 100.

Babban jami’in Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya Mista Mitthias Schmale ne ya bayyana hakan a yayin gabatar da rahotun Tattalin Arziki na Afirka na wannan shekarar (ERA 2023).

Rahoton ya bayyana Annoban COVID-19 da yakin tsakanin Rasha da Ukraine a matsayin wasu daga cikin manyan dalilai da suka janyo munanan matsalar talauci Afirka.

Kasashe da ke biye da Najeriya a yawan matalauta, a cewar rahoton sun hada da Jamhuriyar Dimokoradiyyar Congo da ke da matalauta mutum miliyan 67, sai Tanzaniya da mutum miliyan 36, sai kuma Habasha mai mutum miliyan 33.

Babban jami’in na U.N wanda msanin tattalin arzikin kasa NOnso Obikili ya wakilta, ya shawarci gwamnatocin kasashen su samar da tsarin shugabanci na gari tare da karfafa habakan masana’antu a matsayin babban tsani na shawo kan matsalar.

A jawabin da ya gabatar, mashawarcin shugaban kasa a kan tattalin arziki, Dokta Tope Fasua ya ce ’yan Najeriya na rayuwa cikin tsarin rashin daidaito inda ake da wagegen giɓi atsakanin mawadata da matalauta.

Daraktan harkokin tattalin arziki da mulki a Hukumar Kula da Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Majalisar Dinkin Duniya (UNECA) Adam Elhiraika ya ce cigaban tattalin arzikin Nahiyar yawanci ya dogara ne kan fitar da abubuwan da ake sarrafawa a masana’antun manyan kasashen duniya.

Sai dai kuma hakan ya fuskanci tasgaro a dalilin a lokacin COVID-19 da kuma yakin da ake fama da shi a tsakanin Rasha da kuma Ukraine a yanzu.

Ya ce akwai bukatar kasashen Afirkan su inganta tsarin gudanar da masana’antunsu ta hanyar inganta fasaharsu a bangarori daban-daban.

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Hangen Dala

Shugaban kasa ya bayar da umarnin bude Boda

Published

on

Shugaban kasa Asuwaju Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin kasar nan.

Cikin sanarwar da ya fitar shugaban ya ce duk wata iyaka dake tsakanin Nigeria da jamhuriyar Nijar a gaggauta bude ta.

Karin bayani na nan tafe…

Continue Reading

Trending