Connect with us

Manta Sabo

An gurfanar da Dahiru mai Hudaddu gaban Kotu a kan zargin wasu laifuka

Published

on

Kotun majistret mai lamba 19 karkashi jagorancin mai shari’a Binta Galadanci, ta fara sauraron wata shari’a wadda ‘yan sanda suka gurfanar da Ahmad Dahiru mai Huddadu, bisa zarginsa da laifin bata suna, kalaman tayar da tunzuri, da kuma yunkurin tayar da hankalin al’umma.

Kunshin tuhumar ya bayyana cewar mai Huddadu ya shiga wata kafar yada labarai ya ci mutuncin Sanatan kano ta tsakiya Rufa’i Sani Hanga.

Zargin dai ya bayyana cewar Ahmad mai Huddadu ya batawa sanatan suna inda ya ce ana barnatar da kudin kano ta tsakiya a kulab, yayinda aka karanta kunshin tuhumar mai Huddadun ya musanta.

Lauyan da yake kare shi ya roki kotun ta bayar da belinsa, inda kotun ta amince ta bayar da belin nasa, akan kudi Naira dubu dari biyu, da mutum biyu da za su tsaya masa daya daga cikinsu na zamto mai matakin albashin gwamnati 12, dayan kuma ya zama mai unguwa ko Dagaci.

Bayan fitowa daga kotun wakilinmu Yusif Nadabo Isma’il ya zanta da wakilin Sanata Rufa’i Hanga, wato Shehu Tijjani Usman, wanda ya ce sun kai Mai Hudaddu kara ne kan wani shiri da suke gabatarwa mai suna Taragon A-A Zaura, da ake cin mutumcin Hanga a ciki.

Ya ci gaba da cewa, a baya-bayan nan Sanata Hanga ya bude ofis domin hidimwata mutane kano ta Tsakiya, amma mai Huddadu yana neman lalata tsarin inda yake bata masa suna.

Shima lauyan mai Haddadu Barrister Yusuf Mustafa ya bayyana cewa, bayan da aka karantawa wanda yake karewa ne ya musa kuma suka nemi belinsa, inda ya ce suna ci gaba da duk mai yiyuwa don cika belin.

Wakilin namu ya rawaito cewa kotun ta sanya ranar 29 ga watan gobe dan ci gaba da zaman.

Manta Sabo

Wata Kotu a Kano ta ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar da ƙaramar hukumar Gwale da wani mutum

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 15 da ke zamanta a Mila Road a jihar Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta ci gaba da saurarar karar da al’ummar unguwar Dorayi Baba unguwar jakada suka shigar da karamar hukumar Gwale, da wani mutun mai suna Alhaji Ibrahim Ƴan Shana.

Tunda fari dai mutanan unguwar sun shigar da karar ne suna zargin karamar hukumar ta Gwale, da cefanar wa Ibrahim ‘yan Shana wani fili mallakin al’ummar unguwar na makaranta, lamarin da su garzaya gaban kotun tun a shekarar 2023, a lokacin shugabancin ƙaramar hukumar da ya shuɗe, suna rokon da ta dawo musu da shi domin a gida makaranta a yankin nasu.

Sai dai a zaman kotun na yau bangaren wadanda ake kara na daya wato karamar hukumar Gwale sun gaza gabatar da martanin su akan karar, inda suka roki kotun da ta sanya wata ranar domin gabatar da martanin nasu.

Wakilimmu Mu’az Musa Ibrahim ya rawaito cewa mai shari’ar ya sanya ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta aike da matashin da ake zargi da kashe matar sa gidan yari a Kano

Published

on

Kotun majistret mai lamba 29 karkashin jagorancin mai Shari’a Talatu Makama, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali.

Matashin mai suna Adamu Ibrahim ana zargin sa ne da laifin hallaka mai ɗakinsa ta hanyar kwantara mata dutsen Guga, a fuskarta a can garin kwanar ɗan gora.

Ƙunshin tuhumar ya bayyana cewar, tun a ranar 9 ga watan 4, wani mai suna Idris Adamu yaje caji ofishin ƴan sanda inda ya shigar da kara akan cewar Adamu Ibrahim ya kashe mai ɗakinsa wadda kuma kanwa ce a wajen mai ƙarar Idris Adamu.

Bayan fitowa daga kotun ne wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’ila, ya zanta wanda ake zargi wanda ya ce tsautsayinya sanya shi aikata hakan.

Shima dan uwan marigayiyar ya bayyana matsayarsu, inda ya roƙi kotun da ta yi musu adalci a shari’ar.

Kotun dai ta sanya ranar 17 ga watan gobe dan a kara gabatar da shi a gaban ta domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending