Connect with us

Manyan Labarai

Gwamnan Kano ya gwangwaje ma’aikatan gidan gwamnatin jihar da kayan abinci da kuɗaɗe

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ce zai ci gaba da gudanar da ayyukan alheri ga ma’aikatan musamman idan suka tsaya tsayin daka a kan ayyukan su na dai-dai.

Injiniya Abba Kabir ya bayyana hakan ne yayin bayar da tallafin kayan abinci na miliyoyin Naira ga ma’aikatan gidan gwamnatin da su ke aiki tare da shi, a wani ɓangare na watan Ramadan mai alfarma.

Bayanin hakan na ƙunshe ne ta cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun babban daraktan yaɗa labaran Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a jiya Lahadi, jim kaɗan da bayar da tallafin kayan abincin.

Daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin abincin sun haɗar da ma’aikata daga matakin aiki na 1 zuwa na 12, haka kuma kayan da aka basu sun haɗar da buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50, da katon macaroni, sai buhun gero mai kwano 10, da kuma kudi N10,000 kowannen su.

Yayin da yake gabatar da kayayyakin cikin yanayi na musamman, gwamnan ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi damar yin hakan da nufin ganin an samu nasara ga ma’aikatan sa a cikin watan Ramadan mai albarka.

A cewar sa, “Yau rana ce ta Musamman a gare ni har ma’aikata na a gidan gwamnati domin na fara cika alkawuran yakin neman zabe da na inganta ayyukan jin dadi ga ma’aikatan gwamnati.” in ji gwamnan”.

Gwamnan Abba Kabir ya ƙara da cewa, dangantakar sa da ma’aikatan ba ta iya siyasa ba ce, a dan haka za su iya yin ra’ayoyin su daban-daban, amma abin da yake buƙata daga gare su shi ne sadaukarwa, aiki tukuru, da addu’a domin su cimma abin da suke yi a fagen aiki.

Daga nan sai ya yi kira gare su da su yi amfani da watan Ramadan ta hanyar yawaita ayyukan ibada tare da yin addu’a ga gwamnati da kasa baki daya Allah ya kawo mana dauki, musamman a wannan lokaci na matsin rayuwa.

Da yake jawabi tun da farko mataimakin gwamnan jihar Kano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yabawa gwamnan bisa wannan karamcin da ya nuna, inda ya bayyana hakan a matsayin irinsa da aka taba samu a jihar.

Har ila yau, Kwamared Abdussalam ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar shirin rabon kayan abincin da su mayar da hankali wajen sadaukar da ayyukansu, tare da rikon amana, da addu’a ga gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf, domin ci gaba da samar da ayyukan alheri ga al’ummar jihar.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending