Connect with us

Manyan Labarai

Aƙalla shaguna 180 ne suka ƙone a gobarar babbar kasuwar jihar Sokoto

Published

on

Rahotanni na bayyana cewa wata gobara da ta tashi a babbar kasuwar jihar Sokoto, ta yi sanadiyyar ƙonewar shaguna da dama a ɓangaren masu sayar da babura da kekuna, da safiyar Litinin ɗin nan.

Shugaban ƙungiyar ƴan mashin reshen jihar ta Sokoto, Garba Muhammad Gwazi, ne ya bayyana hakan a zantwarsa da BBC, ya ce gobarar ta laƙume shaguna ‘180’ na masu sayar da babura a cikin kasuwar.

“Sai dai har yanzu ba’a san abin da ya janyo tashin gobarar ba da ta janyo asarar dukiya ta miliyoyin Naira. gobarar ta soma ne daga wata shara da aka tara amma gobarar ba ta kai ga asarar rai ko jikkata kowa ba, “in ji shi”.

Haka kuma Gwazi, ya kuma yi kira ga gwamnati da ta kai musu ɗauki, domin kasuwancin su ya miƙe ya ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

A nasa jawabin mai bai wa gwamnan jihar Sokoto shawara kan babbar kasuwar Honarabul Ibrahim Muhammad Giɗaɗo, ya ce wutar ta tashi da sanyin safiyar yau Litinin.

A cewar sa, “Ɓangaren da ya ƙone sosai a cikin kasuwar shi ne na ƴan babura da kekuna, ana iya samun shago guda ɗauke da mashin fiye da 200 ko 100, shagunan gaba ɗaya sun ƙone,”.

Giɗaɗo ya ƙara da cewa jami’an kashe gobara sun kashe kashi 80 cikin 100 na gobarar da ke ci.

Ya ci gaba da cewa, “Waɗannan baburan akwai waɗanda suka haura miliyan, akwai asara mai yawa.”.

Manyan Labarai

Jarabawar JAMB: An dakatar da duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025 – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da aikin duban tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025, domin bai wa ɗaliban da za su rubuta jarrabawar shiga manyan makarantun kasar nan JAMB, damar isa cibiyoyin zana jarrabawar a kan lokaci.

Kwamishinan muhalli da kula da sauyin yanayi na jihar Kano Dakta Dahir Hashim Muhammad ne ya sanar da hakan, a cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar Sama’ila Garba Gwammaja ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce, an dauki wannan matakin ne bayan nazari da tuntubar masu ruwa da tsaki, a kokarin bai wa daliban jihar Kano damar rubuta jarabawarsu ta JAMB, ba tare da wata matsala ba.

“Muna mai tabbatar wa mazauna Kano cewa, dakatarwar duban tsaftar muhallin na wucin gadi ne a iya wannan watan kawai, kuma za a ci gaba da aikin tsaftar muhallin a watan Mayun 2025, “in ji Dr. Ɗahir”

Kwamishinan ya kuma yi kira ga mazauna jihar Kano, da su ba hukuma hadin kai da fahimtar dalilin da ya sa aka yanke wannan hukunci, musamman na ganin cewa ayyukan tsaftar muhalli ba su ci karo da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a jihar ba.

Continue Reading

Manyan Labarai

Babu ɗaga Ƙafa tsakanin mu da Ƴan Daba da masu ƙwacen Waya a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Wayoyin jama’a da kuma daƙile Shaye-shayen kayan maye ta Anty Snaching Phone, ta gargaɗi matasan da suke addabar al’umma da faɗan Daba a cikin birnin jihar Kano, da su ƙauracewa hakan domin ba za su saurarawa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.

Kwamandan rundunar tsaron a jihar Kano Inuwa Salisu Sharaɗa, shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, ya ce duk wanda suka kama da laifi musamman ma na faɗan Daba, ko ƙwacen waya ko kuma sha da dillancin kayan maye, za a ɗauki tsattsauran mataki akan sa.

 

“Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu ƙwacen Wayoyin jama’a, da Faɗan Daba, da kuma masu Sha da dallancin kayan Maye a jihar Kano, kuma duk wanda mu ka kama sai mun miƙa shi gurin da ya dace don ɗaukar Mataki, “in ji Inuwa Sharaɗa”.

 

Ya kuma buƙaci iyaye da su ƙara sanya idanu wajen kula akan shige da ficen ƴaƴan su, ta yadda za su zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a hukunta duk ma’aikacin Shari’ar da aka samu da laifi – Babbar Jojin Kano

Published

on

Babbar jojin Kano mai Shari’a Dije Abdu Aboki, ta jaddada cewar kwamitin ladabtarwa na hukumar Shari’a a jihar, zai hukunta duk wani ma’aikaci a tsagin Shari’a matuƙar aka same shi da laifin cin-hanci da rashawa.

Mai Shari’a Dije Aboki ta bayyana hakan ne a yayin taron ƙarawa juna sani wanda hukumar shari’ar ta gudanar ranar Talata, a ɗakin taro na Murtala Muhammad Library da ke Kano.

Taron an shirya shi ne don tunasar da sabbin ma’aikatan Shari’a, akan nauyin da ya hau kan su don mayar da hankali sosai akan batun gujewa cin-hanci da rashawa.

Babbar mai Shari’ar Dije Abdu Aboki, ta bayyana cewar akwai takaddu masu ɗauke da lambobin wayarta da aka liƙe a bangon kotuna, kuma duk wanda aka yi wa ba dai-dai ba zai iya sanar da ita ta kan lambobin kuma za a dauki mataki akan duk ma’aikacin da aka samu da laifi.

Wakilin tashar Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, a yayin taron taron ma’aikatan Shari’a da al’umma da dama ne suka samu damar halarta.

Continue Reading

Trending