Connect with us

Manta Sabo

Kotun ɗaukaka ƙara ta yi watsi da ƙarar Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, ta tabbatar wa iyalan Sharu Ilu Rami a Kano

Published

on

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zamanta a sakatariyar Audu Baƙo a jihar Kano, ta yi hukunci akan shari’ar da dattijon nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata ya ɗaukaka, akan wani babban rami da aka yi taƙaddama akansa da ke unguwar Gwammaja a jihar.

Tunda fari dai dattijon ya ɗaukaka ƙarar ne akan hukuncin da babbar kotun kotun jaha ƙarkashin mai Shari’a Justice Usman Na Abba, ta yi, inda ta mallaka wa iyalan marigayi Sharu Ilu ramin, lamarin da dattijon ya ɗaukaka ƙarar.

Sai dai kuma a zaman kotun na yau Laraba, alkalin da ya jagoranci yanke hukuncin a kotun ɗaukaka ƙarar Justice U-A Musalli, ya kori ƙarar dattijon, tare kuma da tabbatar da hukuncin kotun ƙasa, ma’ana dai a baiwa magada iyalan marigayi Sharu Ilu ramin kamar yadda aka yi hukuncin baya a kotun ƙasan.

Bayan fitowa daga kotun ne wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u, ya yi duk mai yiyuwa dan ji daga ɓangaren lauyar Dattijo Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, mai suna Veronika, sai dai ta ce ba abinda za ta ce, a nan ne ya wai-wayi guda daga cikin lauyoyin waɗanda akayi ƙara mai suna Yahya Y Sharif, wanda ya ce daman haka suka yi tsammani, kuma gashi gaskiya tayi halin ta.

Daga bisani dai kotun ta ce a shirye take da ta baiwa kowanne bangare kwafin hukuncin, kuma duk wanda bai gamsu da hukuncin ba yana da dama ya wuce kotun gaba.

Aƙalla dai an shafe sama da shekaru biyar ana taƙaddamar ramin dake unguwar Gwammaja a Kano.

Manta Sabo

Wata Kotu a Kano ta ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar da ƙaramar hukumar Gwale da wani mutum

Published

on

Babbar kotun jaha mai lamba 15 da ke zamanta a Mila Road a jihar Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Sunusi Ado Ma’aji, ta ci gaba da saurarar karar da al’ummar unguwar Dorayi Baba unguwar jakada suka shigar da karamar hukumar Gwale, da wani mutun mai suna Alhaji Ibrahim Ƴan Shana.

Tunda fari dai mutanan unguwar sun shigar da karar ne suna zargin karamar hukumar ta Gwale, da cefanar wa Ibrahim ‘yan Shana wani fili mallakin al’ummar unguwar na makaranta, lamarin da su garzaya gaban kotun tun a shekarar 2023, a lokacin shugabancin ƙaramar hukumar da ya shuɗe, suna rokon da ta dawo musu da shi domin a gida makaranta a yankin nasu.

Sai dai a zaman kotun na yau bangaren wadanda ake kara na daya wato karamar hukumar Gwale sun gaza gabatar da martanin su akan karar, inda suka roki kotun da ta sanya wata ranar domin gabatar da martanin nasu.

Wakilimmu Mu’az Musa Ibrahim ya rawaito cewa mai shari’ar ya sanya ranar 5 ga watan Yunin shekarar 2024 domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta aike da matashin da ake zargi da kashe matar sa gidan yari a Kano

Published

on

Kotun majistret mai lamba 29 karkashin jagorancin mai Shari’a Talatu Makama, ta aike da wani matashi gidan gyaran hali.

Matashin mai suna Adamu Ibrahim ana zargin sa ne da laifin hallaka mai ɗakinsa ta hanyar kwantara mata dutsen Guga, a fuskarta a can garin kwanar ɗan gora.

Ƙunshin tuhumar ya bayyana cewar, tun a ranar 9 ga watan 4, wani mai suna Idris Adamu yaje caji ofishin ƴan sanda inda ya shigar da kara akan cewar Adamu Ibrahim ya kashe mai ɗakinsa wadda kuma kanwa ce a wajen mai ƙarar Idris Adamu.

Bayan fitowa daga kotun ne wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’ila, ya zanta wanda ake zargi wanda ya ce tsautsayinya sanya shi aikata hakan.

Shima dan uwan marigayiyar ya bayyana matsayarsu, inda ya roƙi kotun da ta yi musu adalci a shari’ar.

Kotun dai ta sanya ranar 17 ga watan gobe dan a kara gabatar da shi a gaban ta domin ci gaba da shari’ar.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending