Connect with us

Kasuwanci

KAFADA ku kula da mutanen da ku ke baiwa haya ko sayar da fili ko Gida – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci masu hada-hadar Kasa da Gidaje, da su ƙara himma wajen kula da mutanen da suke bai wa hayar Gidaje ko kuma sayar musu, domin gujewa bada hayar ko kuma sayar wa masu laifi, wanda hakan ka iya taimaka wajen magance matsalar tsaro a ɓangaren.

Kwamishinan ma’aikatar kasuwanci da zuba hannun jari na jihar Kano Alhaji Adamu Aliyu Kibiya, ne ya bayyana hakan yayin ziyarar da tawagar ƙungiyar masu hada-hadar Ƙasa da sayar da Gidaje da kuma bayar da hayar su ta jihar Kano KAFADA, suka kai masa ranar Alhamis a ofishin sa.

Kibiya, ya kuma ce kula da waɗanda za su rinka bai wa hayar gidajen da kuma siyar musu zai taimaka wajen magance matsalar tsaro a sassan jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

Da yake nasa jawabin shugaban kungiyar ta KAFADA, Alhaji Isah Jibril Isah, mai lakabin Kaci-Kasa, ya ce sun kai wa kwamishinan ziyarar ne, domin gabatar masa da kungiyar, da kuma tabbatar masa da hadin kan da za su bashi domin kara bunkasa harkokin kasuwanci a faɗin jihar Kano.

“A shirye kungiyar mu take wajen tabbatar da mambobin mu suna kula da irin mutanen da za su bai wa hayar gida ko kuma sayar musu, domin bada gudunmawar mu ga gwamnati wajen magance matsalar tsaro a jihar Kano, da ma ƙasa baki ɗaya, “in ji shi”.

Alhaji Isah Jibril Isah, ya kuma kara da cewa za su ci gaba da kokari wajen
tsaftace harkokin hada-hadar kasa da sayar da gidaje da bada hayar su, tare da ƙoƙarin ɗaukar mataki akan gurɓatattun mutanen da suke kiran kan su a matsayin dillalai suna
damfarar mutane.

Kasuwanci

Yadda kayan Miya suka yi tashin gwauron Zabi a Kano

Published

on

Wani mai sayar da kayan miya a jihar Kano ya ce yanzu haka kayan miya ya yi tashin gwauron Zabi, lamarin da ke haifar da koma baya a sana’ar tasu.

A zantawar mai kayan miyar da Dala FM Kano, ya ce ko a yau sun sayi buhun tattasai a kan Naira dubu 44, yayin da kwandon Tumatur kuma ya kai Naira dubu 70, inda suka sayi Attaruhu duk buhu kore dubu sittin, sai kuma jan Attaruhu buhu Naira dubu 80.

Malam Musa mai kayan miya ya ƙara da cewar tsadar kayan miyan yana da alaƙa ne da ƙarin kuɗin sufuri da aka samu, da kuma janye tallafin man fetur tunda masu noman rani suna amfani da inji wanda shi kuma fetur ake zuba masa.

Shima wani magidanci da ya je sayan kayan miya ya shaidawa Dala FM Kano, cewa, ya sayi Tattasai kowanne ɗaya akan Naira Ɗari, yayin da ya sayi Tumatur a kan kudi Naira saba’in-saba’in, sai kuma Attaruhu kore Naira goma duk guda ɗaya, yayin da ya sayi jan Attaruhu a kan guda biyu Hamsin.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewar, mutane da dama ne suka rinƙa zuwa sayan kayan miya a wajen mai kayan miyar da ya je wajen sa, sai dai kuma da zarar an basu sai su tafi suna guna-guni da cewar ya yi musu tsada.

Continue Reading

Kasuwanci

Da sana’ar siyar da Awara a bakin Titi na sayi Fili, na gina Gida, kuma nake shirin yin Aure a Kano – Mai lalurar Kafa

Published

on

Wani matashi mai lalurar Kafa da ya rungumi sana’ar siyar da Awara a gefen titin Madobi mai suna Yusif Ibrahim mazaunin Damfami dake karamar hukumar Kumbotso ya shawarci Matasa da su tashi tsaye wajen riko da kananan sana’o’i domin su dogara da kansu.

Matashin mai lalurar kafar ya bayyana hakan ne yayin zantawarsa da wakikinmu na ‘yan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, yana mai cewa riko da sana’ar na taimakawa mutum ya dogara da kansa, tare da magance wasu matsaloli da suke damunsu na yau da kullum.

“Sana’ar siyar da Awarar da nake yi da ita na sayi Fili, na gina Gida, yanzu haka kuma ina shirin yin Aure; Ina ganin budi dan haka akwai bukatar sauran matasa su nemi abin yi ko da sana’ar siyar da Awara ne, “in ji shi”.

Matashin ya kara da cewa akwai kalubale a sana’ar amma dai nasarorin sun fi yawa.

Continue Reading

Kasuwanci

Rashin tallafa mana na kawo nakasu a sana’ar mu – Masu yafin kayan lambu

Published

on

Sakatariyar kungiyar mata masu sana’ar yafin Iraruwan kayan lambu na yankin garin Ali dake karamar hukumar Garko Kubra Hassan, ta ce tallafawa masu yafin irin da abubuwan da suka sawwaka, zai taimaka musu wajen wadata kasar nan da kayan lambu ba sai an shigo da su daga kasashen ketare ba.

Kubra Hassan ta bayyana hakan ne yayin zantawarta da wakilinmu na ‘yan Zazu Hassan Mamuda Ya’u, tana mai cewa yanzu haka mata sun rungumi aikin yafin iraruwan kayan lambun, amma rashin tallafa musu daga bangaren gwamnati shine babban kalubalensu wanda hakan kan kawo musu koma baya a sana’ar tasu.

“Mata ku tashi tsaye wajen rungumar kananan sana’o i domin ku dogara da kan su, tare da taimakawa kanku da ma mazajenku a gidan aure, “in ji Kubra,”

Kubra Hassan ta kuma kara da cewa, babban burinsu shine wadata kasar nan da kayan lambu mai-makon ace an dogara da na kasashen ketare.

Continue Reading

Trending