Connect with us

Manyan Labarai

Mutane 6 sun rasu daga cikin 14 da wani ginin Bene ya danne a Kano

Published

on

Wani ginin Bene mai hawa ɗaya da ake ginawa a unguwar Kuntau kusa da layin Uba Safiyanu, da ya ruguzowa mutane sama da 13, an yi zargin ya yi sanadiyyar rasuwar mutane shida, ciki kuwa har da mai gidan da kuma mai aikin ginin.

Ginin benen dai mai hawa ɗayan ya ruguzo ne a wannan rana ta Juma’a, a dai-dai lokacin da wasu mutane da dama suka fakewa ruwa a jikin gidan, al’amarin da ya danne akalla mutane sama da 13, wanda ya yi sanadiyyar mutane da dama.

Dagacin Dorayi Babba Mallam Musa Badamasi, ya bayyanawa wakilin mu
Mu’azu Musa Ibrahim cewa, a gaban sa an zaƙulo aƙalla mutane 12 daga cikin baraguzan ginin, inda tuni mamallakin gidan da kuma mai aikin gidan suka rasu, inda aka kai su Asibiti.

Dagacin ya kuma shawarci al’umma da su rinƙa neman shawarwarin masana
aikin Gini, a duk lokacin da za suyi gini, ta yadda za’a kaucewa fuskantar matsala irin wacce aka samu.

Yanzu haka dai ana ci gaba da fargaba yayin da ake ci gaba da bada agajin gaggawa a wajen, domin tonon sauran wadanda ginin ya danne.

Idan dai ba’a manta ba ko a kwanakin baya, sai da aka samu ruguzowar
wani ginin Bene a unguwar ta Kuntau al’amarin da ya yi sanadiyyar rasuwar mutane da dama, inda ko a ranar Alhamis, ma sai da aka samu ruguzowar wani ginin Bene mai hawa uku da ake ginawa a unguwar Sharada kwanar kasuwa, amma bai danne kowa ba.

Akan al’amarin ne wakilin Dala FM Kano, Abubakar Sabo, ya tuntuɓi mai magana da yawun hukumar tsara birane ta jihar Kano, KNUPDA, Bahijja Mallam Kabara, ta wayar tarho, sai dai kawo yanzu haƙar sa bata cimma ruwa ba, kasancewar bai ji daga gare ta ba.

Manyan Labarai

An yi jana’izar Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Ahmadu Haruna Zago

Published

on

Ɗaruruwan mutane ne suka halarci sallar jana’izar shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Alhaji Ahmadu Haruna zago, wanda aka gudanar a kofar kudu a fadar mai martaba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu.

Babban kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, shine ya jagorancin sallar jana’izar a tsakar ranar Alhamis ɗin nan.

Daga cikin manyan manyan mutane da Suka hallarci sallar jana’izar marigayin Alhaji Ahmadu Haruna zago, akwai gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, da tsohon kwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwakwanso, da mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, da sauran manyan mutane ciki har da masu riki da mukaman gwamiti.

Da safiyar Alhamis ɗin nan ne dai marigayi Ahmadu Zago, mai shekaru 74 ya rasu, a Asibitin Aminu Kano, bayan fama da rashin lafiya, kafin rasuwar sa yana da mata huɗu da ƴaƴa 37, da jikoki da dama.

Mai martaba sarkin kano Khalifa Muhammadu Sunusi na yayi addu’ar fatan Allah ya jikan marigayin ya kuma baiwa iyalansa da al’ummar jihar Kano jure rashin.

Tuni dai gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya miƙa saƙon ta’aziyyar sa ga al’ummar jihar da kuma iyalan marigayi Ahmadu Haruna Zago, tare da fatan Allah ya gafarta masa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Majalisar dokokin Kano ta amince da kafa rundunar tsaro mallakin jihar

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar kafa Rundunar tsaro mallakin gwamnatin jiha, bayan ɗaukar tsawon lokaci ana dambarwa a majalisar kan saɗarar dokar da ya ce ba’a yarda wanda yake riƙe da katin shaidar kowace jam’iyyar siyasa ba ya shugabanci rundunar tsaron.

Majalisar ta amince da samar da dokar ne bayan shafe kusan fiye da tsawon awa ɗaya ana muhawara akan da yawa daga cikin tanadin da dokar samar da rundunar tsaron ya yi kafin ayi mata karatu na uku.

Da yake ƙarin bayani akan kunshin dokar, Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Husani Dala, ya ce sun yi cikakken Nazari da hangen nesa kafin yin dokar wadda zata taba kowane bangare na jihar Kano wajen daukar ma’aikatan ta musamman wadanda basu da alaka da harkar siyasa.

“Dokar da muka samar ta amincewa jami’an rundunar tsaron ta jihar Kano da za a kafa su ɗauki kowane irin makami domin gudanar da ayyukan su, wanda ya haɗa da kamawa, hana aikata laifi da fatattakar masu aikata laifuka a fadin jihar Kano, “in ji Dala”.

Ditective Auwal Bala Durumin Iya guda daga cikin masana harkokin tsaro ne a ƙasar nan, ya ce akwai buƙatar abi ƙa’idoji wajen ɗaukar jami’an da za su gudanar da aikin rundunar tsaron da zarar gwamnan Kano ya sanya hannu a kan dokar.

A dai zaman na ranar Talata 04 ga watan Fabrairun 2025, majalisar dokokin Kano ta kuma amince da yin gyara akan dokar hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar nan, da hukumar da ke kula da sufuri a kwaryar birnin kano domin samun damar nada musu mataimaka.

Continue Reading

Manyan Labarai

Za’a fara cin tarar Naira dubu 25 akan masu tofar da Yawu ko Majina, ko zubar da Shara ba bisa ƙa’ida ba a Kano

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi dokar cin tarar Naira dubu 25 ga duk wanda aka kama da tofar da Yawu, da Majina, yin Bahaya ko zubar da Shara a sha tale-tale da kuma karkashin gadojin dake Kano.

Wannan ya biyo bayan dokar da majalisar ta Samar wadda za ta gudanar da ayyukan hukumar ƙawata birnin Kano da Kula da wuraren shaƙatawa.

Da yake Karin bayani ga manema labarai, Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala, ya ce ya zama wajibi gwamnati ta dauki matakan da za su tsaftace Kano domin shigar da jihar sahun biranen duniya a fannin tsafta da cigaba.

“Bayan tarar ta Naira dubu 25, akwai kuma sauran hukunce-hukunce da dokar ta tanada wadanda za’ayi amfani dasu wajen ladabtar da duk wanda aka samu da laifukan, “in ji Lawan Dala”.

Majalisar ta kuma yi karatu na biyu kan gyaran dokar hukumar kwashe Shara da tsaftar Muhalli ta Kano domin Samar da mataimakin Shugaba.

Continue Reading

Trending