Connect with us

Labarai

Ku kasance masu neman Ilmi domin sanin kan ku – Human Right

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta buƙaci al’umma da su tashi tsaye wajen neman Ilmi ta yadda za su san kan su, tare da sanin hanyoyin da ake bi wajen neman haƙƙi yayin da aka danne musu.

Babban jami’in gudanarwar ƙungiyar Kwamared Tasi’u Idris Idris (Soja) ne ya bayyana hakan yayin ganawar sa da manema labarai, a wani ɓangare na taron ƙarawa juna sani akan aikace-aikacen ƙungiyar da ma abinda ya shafi hulɗa da jami’an tsaro, da ƙungiyar ta gudanar ranar Lahadi a Kano.

Kwamared Tasi’u Idris ya kuma ce a shirye ƙungiyar tare wajen ƙara kyautata alaƙar ta da jami’an tsaro, domin ganin an ci gaba da gudanar da ayyukan al’umma cikin nasara ba tare da fuskantar matsala ba.

Da yake nasa jawabin masanin tsaron nan Ditective Auwal Bala Durumin Iya, shawartar ƴan ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ya yi, da su ƙara himma wajen neman ilmin aikin da suke yi, wanda hakan ka iya taimaka musu wajen kaucewa fuskantar matsala.

Shima a nasa ɓangaren Dagacin garin Sharaɗa Alhaji Ilyasu Mu’azu Sharaɗa, kira ya yi ga ƴan ƙungiyar da su ƙara da kiyaye dukkanin abinda ka iya haifar musu da matsala yayin gudanar da ayyukan su.

Majiyar Dala FM Kano ta rawaito cewa yayin taron al’umma da dama ne suka samu damar halarta, kuma ciki har da Kakakin rundunar tsaro ta Civil Defense SC Ibrahim Idris Abdullahi, wanda ya samu Wakilcin mataimakin sa AS Abdulmajeed, da ƴan ƙungiyar

Addini

Hajji2025: Maniyyatan Najeriya 16,182, sun sauka a Saudiyya – NAHCON

Published

on

Hukumar kula da Alhazai ta Najeriya, NAHCON, ta ce izuwa yanzu aƙalla maniyyatan ƙasar su 16,182, ne suka sauka a ƙasar Saudiyya, domin gudanar da aikin Hajjin bana na shekarar 2025.

Hukumar ta NAHCON, ta bayyana hakan ne da yammacin Alhamis ɗin nan a shafinta na Facebook, ta ce aƙalla jirage 40, ne suka yi jigilar maniyyatan, daga ranar juma’ar da ta gabata, da aka fara kai maniyyatan zuwa ƙasa mai tsarki.

 

NAHCON, ta ƙara da cewa, jirgi na ƙarshe da ya sauka a Madinah, shi ne jirgin UMZA, mai lamba UMZ3412, da ya tashi ɗauke da maniyyatan jihar Kaduna su 299, Maza 229, mata kuma 70, sai wasu na musamman su 9.

Continue Reading

Labarai

Rashin taimaka wa masu buƙata ta musamman ya sa suke barace-barace – Sarkin Dawakin Makafin Kano

Published

on

Sarkin Dawakin Makafin Kano Abubakar Ibrahim Gwarzo, ya ce samar wa masu buƙata ta musamman guraben aiki ka iya taimaka musu wajen ficewar su daga yawaitar barace-barace a tsakanin al’umma.

Abubakar Ibrahim Gwarzo, na wannan jawabin ne a yayin da gidauniyar tallafawa masu buƙata ta musamman da mabuƙata ta Marigayi Farfesa Jibril Isah Ɗiso, ta bai wa masu lalurar gani su 25, tallafin Kuɗi aƙalla Naira dubu goma goma, da dubu ashirin-ashirin ga kowannen su, a Firamaren Dala da ke unguwar Makafin Dala, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.

“Duba da yadda masu bukata ta musamman suke da kaifin basira, akwai buƙatar a rinƙa samar musu guraben ayyukan yi domin su dogara da kan su, “in ji Gwarzo”.

Abubakar Ibrahim, ya kuma shaidawa Dala FM Kano, cewa, masu buƙata ta musamman suna cikin wani hali mawuyacin hali, musamman ma da rashin taimaka musu yake sanya ake samun wasu na yin barace-barace a tsakanin al’umma.

“Masu lalurar gani suna iya ƙirga abubuwa, kamar irin su Sabulu, da yin sauran abubuwa, idan aka dauke su aiki hakan zai taimaka musu tare da kaucewa faɗawar su a cikin barace-barace, “in ji shi”.

Gwarzo, ya kuma yi kira ga gwamnan jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ya tuna da alkawarin da ya yi musu a lokacin yaƙin neman zaɓen sa, kan taimaka wa masu buƙata ta musamman idan ya samu nasara, lamarin da ya ce zuwa yanzu ya ci tura, a don haka suke kira ga gwamnan da ya kai musu ɗauki.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kano ta biya sama da Biliyan uku don biyawa ɗalibai kuɗin jarabawar Qualifying a jihar

Published

on

Gwamnatin Kano ta amince da kashe aƙalla sama da Naira Biliyan dubu ɗaya, don biya wa ɗaliban jihar kuɗin jarabawar neman shiga makarantun gaba da Sakandire ta NECO, domin sauƙaƙa musu a fagen karatunsu.

Kwamishinan Ilmi na jihar Kano Dakta Gwani Haruna Makoɗa, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da manema labarai a ranar Juma’a, ya ce ɗalibai 141,715, ne suka rubuta jarabawar neman cancantar ta samun damar rubuta jarabawar NECO, kyauta, daga gwamnatin, ko kuma ɗalibi ya biya da kan sa kuɗin jarabawar da akafi sani da Qualifying.

A cewar sa, “Ɗaliban da suka samu nasarar gami da cancanta da za a biyawa kuɗin daga gwamnatin Kano, sun samu sakamako biyar zuwa sama ne ga kowanne su, kuma kaso saba’in da biyar cikin ɗari na ɗaliban sun samu nasara, “in ji Gwani Makoɗa”.

Kazalika, Makoɗa, ya kuma ce wannan na daga cikin ƙudirin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin haɓaka ilmi da ƙara haɓaka tattalin arziki, da kuma tallafawa karatun Ɗalibai musamman ma Matasa, da taimaka wa Iyaye a faɗin jihar, lamarin da ya ce Abba ya cika Gwarzo wajen kula da ilmi da sauran ɓangarori a Kano.

 

Tashar Dala FM Kano, ta ruwaito cewa, Kwamishinan na ilmi a Kano Gwani Ali Haruna Makoɗa, ya kuma buƙaci shugabannin makarantun gwamanti a jihar, da su tabbatar da cewar kowanne ɗalibi ya cancanci sanin sakamakon sa ba tare da wani sharaɗi ba.

Continue Reading

Trending