Labarai
Ku guji tada hankalin al’umma yayin zaɓen ƙananan hukumomi a Kano – Human Right

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta buƙaci al’umma musamman ma Matasa da su kasance masu bin doka da oda tare kuma da gujewa tayar da hankalin jama’a a yayin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin da za ayi a yau Asabar.
Shugaban gudanarwar ƙungiyar na Ƙasa Kwamared Tasi’u Idris Idris (Soja) ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a safiyar Asabar.
Ya kuma ce bai kamata al’umma su kasance masu taka doka ba, domin bin doka shi ne wayewa.
“Muna kuma kira ga jami’an tsaro da su bada gudunmawar su yayin zaɓen domin ganin an gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin cikin kwanciyar hankali, “in ji Tasi’u”.
Da yake nasa jawabin daraktan ƙungiyar Kwamared Gambo Madaki, kira ya yi ga dukkanin ƴan ƙungiyar su na ƙananan hukumomin Kano 44, da ku guji sanya kayan ƙungiyar su yayin gudanar da zaɓen kasancewar ba sa cikin masu aikin zaɓen ko kuma sanya ido, domin gujewa fuskantar matsala.
Tuni dai hukumar zaɓe ta jihar Kano Kanseic, ta ce za’a fara kaɗa ƙuri’a ne da misalin ƙarfe takwas na safiyar yau Asabar.

Addini
Hajji2025: Maniyyatan Najeriya 16,182, sun sauka a Saudiyya – NAHCON

Hukumar kula da Alhazai ta Najeriya, NAHCON, ta ce izuwa yanzu aƙalla maniyyatan ƙasar su 16,182, ne suka sauka a ƙasar Saudiyya, domin gudanar da aikin Hajjin bana na shekarar 2025.
Hukumar ta NAHCON, ta bayyana hakan ne da yammacin Alhamis ɗin nan a shafinta na Facebook, ta ce aƙalla jirage 40, ne suka yi jigilar maniyyatan, daga ranar juma’ar da ta gabata, da aka fara kai maniyyatan zuwa ƙasa mai tsarki.
NAHCON, ta ƙara da cewa, jirgi na ƙarshe da ya sauka a Madinah, shi ne jirgin UMZA, mai lamba UMZ3412, da ya tashi ɗauke da maniyyatan jihar Kaduna su 299, Maza 229, mata kuma 70, sai wasu na musamman su 9.

Labarai
Rashin taimaka wa masu buƙata ta musamman ya sa suke barace-barace – Sarkin Dawakin Makafin Kano

Sarkin Dawakin Makafin Kano Abubakar Ibrahim Gwarzo, ya ce samar wa masu buƙata ta musamman guraben aiki ka iya taimaka musu wajen ficewar su daga yawaitar barace-barace a tsakanin al’umma.
Abubakar Ibrahim Gwarzo, na wannan jawabin ne a yayin da gidauniyar tallafawa masu buƙata ta musamman da mabuƙata ta Marigayi Farfesa Jibril Isah Ɗiso, ta bai wa masu lalurar gani su 25, tallafin Kuɗi aƙalla Naira dubu goma goma, da dubu ashirin-ashirin ga kowannen su, a Firamaren Dala da ke unguwar Makafin Dala, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa.
“Duba da yadda masu bukata ta musamman suke da kaifin basira, akwai buƙatar a rinƙa samar musu guraben ayyukan yi domin su dogara da kan su, “in ji Gwarzo”.
Abubakar Ibrahim, ya kuma shaidawa Dala FM Kano, cewa, masu buƙata ta musamman suna cikin wani hali mawuyacin hali, musamman ma da rashin taimaka musu yake sanya ake samun wasu na yin barace-barace a tsakanin al’umma.
“Masu lalurar gani suna iya ƙirga abubuwa, kamar irin su Sabulu, da yin sauran abubuwa, idan aka dauke su aiki hakan zai taimaka musu tare da kaucewa faɗawar su a cikin barace-barace, “in ji shi”.
Gwarzo, ya kuma yi kira ga gwamnan jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ya tuna da alkawarin da ya yi musu a lokacin yaƙin neman zaɓen sa, kan taimaka wa masu buƙata ta musamman idan ya samu nasara, lamarin da ya ce zuwa yanzu ya ci tura, a don haka suke kira ga gwamnan da ya kai musu ɗauki.

Labarai
Gwamnatin Kano ta biya sama da Biliyan uku don biyawa ɗalibai kuɗin jarabawar Qualifying a jihar

Gwamnatin Kano ta amince da kashe aƙalla sama da Naira Biliyan dubu ɗaya, don biya wa ɗaliban jihar kuɗin jarabawar neman shiga makarantun gaba da Sakandire ta NECO, domin sauƙaƙa musu a fagen karatunsu.
Kwamishinan Ilmi na jihar Kano Dakta Gwani Haruna Makoɗa, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da manema labarai a ranar Juma’a, ya ce ɗalibai 141,715, ne suka rubuta jarabawar neman cancantar ta samun damar rubuta jarabawar NECO, kyauta, daga gwamnatin, ko kuma ɗalibi ya biya da kan sa kuɗin jarabawar da akafi sani da Qualifying.
A cewar sa, “Ɗaliban da suka samu nasarar gami da cancanta da za a biyawa kuɗin daga gwamnatin Kano, sun samu sakamako biyar zuwa sama ne ga kowanne su, kuma kaso saba’in da biyar cikin ɗari na ɗaliban sun samu nasara, “in ji Gwani Makoɗa”.
Kazalika, Makoɗa, ya kuma ce wannan na daga cikin ƙudirin gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin haɓaka ilmi da ƙara haɓaka tattalin arziki, da kuma tallafawa karatun Ɗalibai musamman ma Matasa, da taimaka wa Iyaye a faɗin jihar, lamarin da ya ce Abba ya cika Gwarzo wajen kula da ilmi da sauran ɓangarori a Kano.
Tashar Dala FM Kano, ta ruwaito cewa, Kwamishinan na ilmi a Kano Gwani Ali Haruna Makoɗa, ya kuma buƙaci shugabannin makarantun gwamanti a jihar, da su tabbatar da cewar kowanne ɗalibi ya cancanci sanin sakamakon sa ba tare da wani sharaɗi ba.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su