Connect with us

Labarai

Sarkin Kano ya ɗaga likkafar Alhaji Abbas Ɗalhatu daga Ƴan Daka, zuwa Bauran Kano, da naɗa hakimai 10

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Dakta Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya naɗa Alhaji Abbas Ɗalhatu shugaban rukunin gidajen Freedom Radio da Dala FM, a matsayin Bauran Kano, bayan da ya ɗaga likkafar sa daga Ƴan Ɗakan Kano.

Sarkin ya naɗa hakiman ne da safiyar yau Juma’a, inda ya kuma naɗa hakimai goma a matakai daban-daban, daga cikin su akwai Kacallan Kano, da Dan Adalan Kano, da mai unguwar Munduɓawa kuma hakimin Gezawa, da sauransu.

Da yake jawabi jim kaɗan da ɗin hakiman da kuma ɗaga likkar Alhaji Abbas Ɗalhatu zuwa Bauran Kano, mai martaba Sarkin Kano Dakta Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya ce an naɗa hakiman ne bisa jajirecewar su da taimaka wa al’umma da kuma biyayya ga masarautar Kano.

Sarkin na Kano Khalifa Muhammadu Sunusi na biyu, ya kuma hori dukkanin hakiman da su mayar da hankali akan samar da ci gaban al’ummar jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Doragarai ya ruwaito cewa a yayin naɗin al’umma da dama ne suka samu damar halarta daga ciki da wajen ƙasar nan.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

Continue Reading

Trending