Manyan Labarai
Masu Garkuwa da mutanen da muka kama a dajin Ɗansoshiya sun rasu – Ƴan Sandan Kano

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce masu Garkuwa da mutane su biyun da ta kama a dajin Ɗansoshiya da ke kwanar Ɗangora a ƙaramar hukumar Ƙiru a jihar sun rasu.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da hakan a shafin sa na sada zumunta a cikin daren Asabar 09 ga watan Nuwamban 2024.
Tun dai da safiyar Asabar ne rundunar ta ce ta cafke mutane biyun da ta ke zarginsu da shiga jihar Kano, domin yin garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.
SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa, an kama mutanen ne a garin Kwanar Dangora, kuma, suna hannun ‘yan sanda domin fadada bincike, ko da ike yanzu haka tuni suka riga mu gidan gaskiya.
Majiyar Dala FM Kano ta rawaito cewa SP Kiyawa ya kuma ƙara da cewa, yanzu ta’addancin satar mutane ba za ta yi tasiri a Jihar Kano ba da yardar Allah’.
Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan na Kano, ya kuma gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’in da suke yi a kullum.
Tuni dai Kiyawa ya wallafa hotunan gawar mutanen biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a shafin sa na Facebook.

Baba Suda
Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.
Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.
Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.
Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Manyan Labarai
Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.
Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.
Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.
Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Manyan Labarai
Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.
Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su