Connect with us

Manyan Labarai

Za’a fara cin tarar Naira dubu 25 akan masu tofar da Yawu ko Majina, ko zubar da Shara ba bisa ƙa’ida ba a Kano

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi dokar cin tarar Naira dubu 25 ga duk wanda aka kama da tofar da Yawu, da Majina, yin Bahaya ko zubar da Shara a sha tale-tale da kuma karkashin gadojin dake Kano.

Wannan ya biyo bayan dokar da majalisar ta Samar wadda za ta gudanar da ayyukan hukumar ƙawata birnin Kano da Kula da wuraren shaƙatawa.

Da yake Karin bayani ga manema labarai, Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala, ya ce ya zama wajibi gwamnati ta dauki matakan da za su tsaftace Kano domin shigar da jihar sahun biranen duniya a fannin tsafta da cigaba.

“Bayan tarar ta Naira dubu 25, akwai kuma sauran hukunce-hukunce da dokar ta tanada wadanda za’ayi amfani dasu wajen ladabtar da duk wanda aka samu da laifukan, “in ji Lawan Dala”.

Majalisar ta kuma yi karatu na biyu kan gyaran dokar hukumar kwashe Shara da tsaftar Muhalli ta Kano domin Samar da mataimakin Shugaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a Reply

Manyan Labarai

Majalisar dokokin Kano ta amince da kafa rundunar tsaro mallakin jihar

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da dokar kafa Rundunar tsaro mallakin gwamnatin jiha, bayan ɗaukar tsawon lokaci ana dambarwa a majalisar kan saɗarar dokar da ya ce ba’a yarda wanda yake riƙe da katin shaidar kowace jam’iyyar siyasa ba ya shugabanci rundunar tsaron.

Majalisar ta amince da samar da dokar ne bayan shafe kusan fiye da tsawon awa ɗaya ana muhawara akan da yawa daga cikin tanadin da dokar samar da rundunar tsaron ya yi kafin ayi mata karatu na uku.

Da yake ƙarin bayani akan kunshin dokar, Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Husani Dala, ya ce sun yi cikakken Nazari da hangen nesa kafin yin dokar wadda zata taba kowane bangare na jihar Kano wajen daukar ma’aikatan ta musamman wadanda basu da alaka da harkar siyasa.

“Dokar da muka samar ta amincewa jami’an rundunar tsaron ta jihar Kano da za a kafa su ɗauki kowane irin makami domin gudanar da ayyukan su, wanda ya haɗa da kamawa, hana aikata laifi da fatattakar masu aikata laifuka a fadin jihar Kano, “in ji Dala”.

Ditective Auwal Bala Durumin Iya guda daga cikin masana harkokin tsaro ne a ƙasar nan, ya ce akwai buƙatar abi ƙa’idoji wajen ɗaukar jami’an da za su gudanar da aikin rundunar tsaron da zarar gwamnan Kano ya sanya hannu a kan dokar.

A dai zaman na ranar Talata 04 ga watan Fabrairun 2025, majalisar dokokin Kano ta kuma amince da yin gyara akan dokar hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar nan, da hukumar da ke kula da sufuri a kwaryar birnin kano domin samun damar nada musu mataimaka.

Continue Reading

Manta Sabo

Kotu ta yanke wa wasu mutane 5 hukuncin Kisa ta hanyar Rataya a Kano

Published

on

Babbar kotun jihar Kano, mai lamba huɗu karkashin jagorancin mai Shari’a Usman Na Abba, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya akan wasu mutane 5, waɗanda kotun ta samu da laifin haɗa baki da kisan kai.

Tunda fari gwamnatin jihar Kano ce ta gurfanar da mutanen a gaban kotun, da ake zargin su da haɗa baki da kisan kai.

Ƙunshin zargin da ake musu tun da fari ya bayyana cewar, a ranar 3 ga watan 9 na shekarar 2023 wata mata Mai suna Nadiya Ibrahim ta bayyana wa mai gidanta Faisal Yahaya cewar, ta yi mafarkin cewar wata makociyarsu mai suna Tsahare Abubakar ta biyo ta da wuka, bayan da ta farka kuma sai ta kama rashin lafiya.

Har ila yau, ƙunshin tuhumar ya bayyana cewar, Faisal ya yi zargin Tsahare mayyace, don haka ya gayyato wasu matasa 4 su ka bi Tsahare har gona suka daddatsa ta har sai da rai ya yi halinsa.

A yayin sauraron Shaidu lauyan gwamnati Barrister Lamido Abba Soron Ɗinki, ya gabatar da shaidu 4, kuma a yau kotun ta ayyana cewar, ta gamsu da shaidun masu gabatar da kara.

Kotun ta ayyana hukunci kisa ta hanyar rataya akan mutanen masu suna Daluta Ibrahim, da Abudil-Aziz Yahaya, da Faisal Yahaya, da kuma Ahmad Ibrahim, sai Abdurrahman Yakubu.

Sai dai kuma wata mata da ake tuhuma ta 6 mai suna Nadiya Ibrahim, kotun ta sallame ta sakamakon an gano cewar lokacin da aka yi kisan kan ita tana gida a kwance bata da lafiya.

Kazalika, kotun ta kuma gargadi yan uwan Tsahare akan cewar kada su cutar da Nadiya domin kotun ta gano bata da laifi.

Wakilimmu Yusuf Nadabo Isma’il ya ruwaito cewa, kotun ta kuma umarci Dagacin garin Ɗadin kowa da ke karamar hukumar Wudil, da su tabbatar an zauna lafiya akan wannan batu, har ma mai Shari’a Usman Na’Abba ya ce, ba a yin hukunci akan mafarki kuma idan wani ya faru da mutum sai ya tuntuɓi masana abin.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ƙarin Kuɗin Kira: Ƙungiyar ƙwadago ta shirya gudanar da Zanga-zanga a Najeriya

Published

on

Kungiyar ƙwadago ta ƙasa NLC, ta shirta gudanar da zanga-zanga ta kasa a ranar 4 ga watan Fabrairu mai kamawa kan karin kudin kira da Data dana tura sakonni da gwamnatin tarayya ta yi.

Ƙungiyar dai ta amince da yin zanga-zangar ne a yayin taron shugabannin NLC na kasa da ke gudana, a wani ɓangare na nuna takaicin ta kan halin da ƴan Najeriya suka samu kansu a ciki, kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito.

Matakin dai wani jan kunne ne ga gwamnati cewa ma’aikata za su ci gaba da kalubalantar karin kudin saboda yanayin talauci da zai kara jefa al’ummar Najeriya.

Da yake jawabi akan batun shugaban ƙungiyar ƙwadagon na ƙasa Joe Ajaero, ya ce, ƙarin kiran da na Data da kuma na tura saƙonni da aka yi za a iya kiran sa da cin zarafin ma’aikata, kuma tauye wal-walar su.

A cewar sa, ƙarin ya zo ne a dai-dai lokacin da ƴan Najeriya ke fuskantar halin matsayin rayuwa bisa durƙushewar tattalin arziƙi.

Continue Reading

Trending