Connect with us

Labarai

Hukumar Hisbah ta Kano ta yi bikin fasa kwalaben barasa 196,400

Published

on

Hukumar Hisbah ta Kano ta yi bikin fasa kwalaben barasa 196,400

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta fasa kwalaban barasa fiye da dubu daya da casa’in da shida da dari hudu 196, 400 da ta kama a wasu sassan cikin birnin Kano.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwar da babban sakataren yada labaran mataimakin gwamnan jihar Kano Hassan Musa Fagge ya fitar.

Da yake jawabi jim kadan bayan lalata kwalaben a yankin Kalemawa dake karamar hukumar Dawakin Tofa, gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yace addinin musulunci ya haramata shan giya da duk wani nau’in abubuwan dake sa maye.

Abdullaha Umar Ganduje ya yi bayanin cewar addinin musulunci ya yi hani da shan miyagun kwayoyi don gusar da hankali, yana mai yin kira ga malaman addinai da su hada hannu guri guda wajen yaki da shaye-shaye a jihar Kano.

Gwamnan Kano wanda ya sami wakilcin mataimakin sa Nasiru Yusuf Gawuna ya baiwa hukumomin shari’a na jihar kano tabbacin goyan bayan gwamnati wajen yaki da sha da miyagun kwayoyi musamman ma barasa.

Mataimakin gwamnan ya kara da cewa gwamantin Kano za ta cigaba da tallafawa hukumar Hisbah musamman bayan da aka kammala kaddamar da kwamandojin kananan hukumomi 44 na jihar.

Da yake jawabi babban kwamandan Hisbah na jihar Kano Sheikh Haruna Ibni-Sina, ya ce hukumar ta ci nasarar hana saida barasa da shan ta a cikin birnin Kano da kewaye, karkashin sashi na 401 na kudin tsarin shari’ar musulunci.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending