Connect with us

Labarai

Kai tsaye: Lauyoyi suna tattaki a Kano

Published

on

Ku cigaba da bibiya ana sabunta wannan shafi da sabbin bayanai.

12pm

Adai-dai wannan lokaci kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jahar kano suna tattaki zuwa gidan gwamnati dan bada shawarwari da kuma mika koke koke aka Marsala tsaro. Ana yin tattakin karkashin jagoranci shugaban kungiyar M A lawan.

A yau ne kungiyar lauyoyi ta kasa reshen kano NBA karkashin shugabanta barrister Musa Abdullahi Lawan za suyi tatattaki daga sakatariyar su da ke gidan gona a nan Kano zuwa gidan gwamnatin jihar Kano, don bayyana takaicinta da kuma kara zaburar da gwamnati da ta kara rubanya kokarin da takeyi wajen bawa jami’an tsaro hadin kai.

Tattakin zai fara da misalin karfe 10 na safiyar nan.

Kungiyar dai na kukan yadda matsalolin tsaro musamman garkuwa da mutane da fashi da makami da fyade suke kara ta azzara a jahar.

Cikin wata sanarwa da suka fitar makonni biyu da suka gabata NBA Sun bayyana cewar ta wannan hanyar ne kawai za a yi shawo kan matsalolin.

Ana sa ran za ayi kwanaki hudu ana taron wayar da kan al’umma kan wadannan batutuwa, cikin wadanda zas uyi jawabi a yayin taron akwai manyan alkalai daga kotun koli da kuma shaihunnan malamai daga sassa da ban da ban na kasar nan.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il yana sakatariyar NBA a yanzu haka kuma ku kasance da mu dan jin yanda taron zai kasance kai tsaye.

RUBUTU MASU ALAKA:

An sauke masu rike da mukamai a Hisbah

Bikin cika shekara 73 na majalisar dinkin duniya UN.

An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending