Connect with us

Labarai

Covid-19 Kungiyar daliban Tukuntawa TUYODA ta raba sinadarin wanke hannu a masallatai

Published

on

Kungiyar daliban unguwar Tukuntawa TUYODA, da sauran hadin gwiwar kungiyoyin yankin sun dauki gabaran gudanar da rabon sinadarin wanke hannaye a cikin masallatan fadin yankin baki daya.

Kungiyar wadda ta fara daukan wannan matakin a cikin makon nan domin dakile yaduwar annobar cutar Covid-19 a yankin unguwar Tukuntawa dake karamar hukumar  birni da kewaye.

Sinadaren wanke hannuun da kungiyar TUYODA ta hada

Yayin rabon sinadarin wanke hannayen, Sakataren kungiyar, Zahradeen Usaini Lizarazu, ya ce ”Muna bin layi-layi na fadin unguwar domin wayar da kan al’umma cewa wannan cuta ta Coronavirus gaskiya ce domin haka muka gayyato mai hada magunguna ya kuma koya mana yadda a ke hada sinadarin wanke hannu, kuma muna bi masallatai da loko-loko na unguwar mu na rabawa domin kare kai”.

A nasa jawabin shugaban kungiyar TUYODA, Fardeen Aliyu, cewa ya yi” Muna wayar da kan mu ne kafin a ce wata kungiya ta zo ta taimaka mana daga waje, saboda haka mu ka hadu muka kirawo sauran kungiyoyin mu na cikin unguwa domin wayar da kan al’umma wajen wanke hannayen mu kafin mu ci abinci ko taba wani abu, domin haka muka kirawo guda daga cikin me hada magunguna ya koya mana muka kuma hada mu ke bi cikin masallatai domin raba wannan abun wanke hannun, harma mu bi inda majalisa take mu raba masu”.

Shi kuwa mai hada maganin, Pharmacist Auwal Bala, inda ya ce” A matsayi nan a mazaunin unguwar Tukuntawa mun zauna mun dauki wannan matakin ne domin hada wannan sinadarin wanke hannu kuma wanda kungiyar lafiya ta duniya ta amince da shi, domin ita ta bayyana yadda zamu hada shi cikin sauki wanda mutum zai iya hadawa a gida kuma ga shi da kudi kadan muka hada saboda wancan ya yi tsada, saboda haka muke kira da masu hannu da shuni da sauran al’umma da su tashi tsaye wajen bada tallafi ga irin wadannan kungiyoyi domin su hada su kuma rabawa al’umma”.

Guda daga cikin wanda suka rabauta da sinadarin wanke hannun’ Rabi’u Abdullahi Abubakar Tukuntawa ya ce” Sai dai mu yi godiya ga wannan kungiya sakamakon dama mu bamu dashi sai dai mu wanke hannu da ruwan kumfa kuma tabbas mun ji dadin wannan batu na wayar da kai da TUYODA take yi a Tukuntawa” A cewar mazaunin unguwar.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending