Labarai
Covid-19 Kungiyar daliban Tukuntawa TUYODA ta raba sinadarin wanke hannu a masallatai
Kungiyar daliban unguwar Tukuntawa TUYODA, da sauran hadin gwiwar kungiyoyin yankin sun dauki gabaran gudanar da rabon sinadarin wanke hannaye a cikin masallatan fadin yankin baki daya.
Kungiyar wadda ta fara daukan wannan matakin a cikin makon nan domin dakile yaduwar annobar cutar Covid-19 a yankin unguwar Tukuntawa dake karamar hukumar birni da kewaye.
Yayin rabon sinadarin wanke hannayen, Sakataren kungiyar, Zahradeen Usaini Lizarazu, ya ce ”Muna bin layi-layi na fadin unguwar domin wayar da kan al’umma cewa wannan cuta ta Coronavirus gaskiya ce domin haka muka gayyato mai hada magunguna ya kuma koya mana yadda a ke hada sinadarin wanke hannu, kuma muna bi masallatai da loko-loko na unguwar mu na rabawa domin kare kai”.
A nasa jawabin shugaban kungiyar TUYODA, Fardeen Aliyu, cewa ya yi” Muna wayar da kan mu ne kafin a ce wata kungiya ta zo ta taimaka mana daga waje, saboda haka mu ka hadu muka kirawo sauran kungiyoyin mu na cikin unguwa domin wayar da kan al’umma wajen wanke hannayen mu kafin mu ci abinci ko taba wani abu, domin haka muka kirawo guda daga cikin me hada magunguna ya koya mana muka kuma hada mu ke bi cikin masallatai domin raba wannan abun wanke hannun, harma mu bi inda majalisa take mu raba masu”.
Shi kuwa mai hada maganin, Pharmacist Auwal Bala, inda ya ce” A matsayi nan a mazaunin unguwar Tukuntawa mun zauna mun dauki wannan matakin ne domin hada wannan sinadarin wanke hannu kuma wanda kungiyar lafiya ta duniya ta amince da shi, domin ita ta bayyana yadda zamu hada shi cikin sauki wanda mutum zai iya hadawa a gida kuma ga shi da kudi kadan muka hada saboda wancan ya yi tsada, saboda haka muke kira da masu hannu da shuni da sauran al’umma da su tashi tsaye wajen bada tallafi ga irin wadannan kungiyoyi domin su hada su kuma rabawa al’umma”.
Guda daga cikin wanda suka rabauta da sinadarin wanke hannun’ Rabi’u Abdullahi Abubakar Tukuntawa ya ce” Sai dai mu yi godiya ga wannan kungiya sakamakon dama mu bamu dashi sai dai mu wanke hannu da ruwan kumfa kuma tabbas mun ji dadin wannan batu na wayar da kai da TUYODA take yi a Tukuntawa” A cewar mazaunin unguwar.
Labarai
Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama
Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.
Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.
Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.
Labarai
Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam
Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.
Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.
Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.
Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.
Labarai
Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.
Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.
Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.
Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.
Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.
Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su