Connect with us

Labarai

covid-19: Zaman gida ya sa kasuwar Tuwo ta yi daraja a Kano

Published

on

Wani magidanci ya budewa ‘yan uwansa magidanta, majalisar cin sabon Tuwo da rana a yankin Sharada, inda al’umma da dama su ke halartar wajen domun cin Tuwon, kasancewar a na zaune a gida kuma wasu basu da abun da za a ci a gidajen su.

A cikin majalisar har da wani Bafulatani da ya ce, “Yanzu fura ba a za zancen ta domin ta tuwo a ke yi yayin di ba”.

Ya kuma ce, “Tun daga Farawa na ke hawa motar domin kwaikwaiyo na zo na ci sabon tuwon na fisabilillahi a wannan majalissa, na kuma bar ‘ya’ya na takwas gida babar su ta yi ‘yan make-make ta ba su, ni kuma na zo na dame cikina ya koma”. A cewar Bafulatani.

Kazalika, shima wani magidancin ya ce, “Nima nawa ‘ya’yan goma sha biyu nake barin su a gida in kuma taho tun daga unguwar Samegu in debi tuwon in koma gida”.

Sai dai wanda ya bude majalissar ciyar da magidantan saboda tuwon dawa na rana fisabilillahi, ya ce, “A’a ba zai iya ciyar musu da iyalan na su ba, suma kuma ya ciyar da su”. Inji mai tuwon majalisa.

Magidan cin ya dai bude sabuwar majalisar ne a yankin unguwar Sharada dake karamar hukumar birni a lokacin da a ke kulle a jihar Kano domin bada gudunmawar sa wajen ciyar da abokai abinci.

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending