Connect with us

Labarai

Magidanci ya yi wa matar sa dukan kawo wuka a kan sallah

Published

on

Wani magidanci mai suna Muhammad Rabi’u dake unguwar Bachirawa a yankin Darerawa, karamar hukumar Fagge, ana zarginsa da yiwa matarsa Maryam dukan kawo wuka a cikin dare saboda ta yi masa nasiha akan ya rinka yin sallah.

Wakilin mu Abubakar Sabo ya zanta da wani makwabcin magidancin, wanda suka kubutar da matar ya ce, “Muna kofar gida sai naga mace ta fito kusan babu kaya a jikinta, sai naje muka shiga cikin gida aka bata kaya ta saka”. A cewar Makwabcin Magidancin.

Itama wata makwabciyar ma’auratan, ta bayyana yadda al’amarin ya faru, “Mu dai muna cikin gida muka rinka jin ihu, sai muka ce ko wata ce ta tayar da aljanu, muna fitowa sai muka ga mace daga ita sai siket, ta na cewa, mjinta ne yake ikirarin sai ya kashe ta, saboda ta ce yayi sallah, sai mu ka ce ta shigo aka bata kaya ta saka”. Inji Makwabciyarsu.

Kazalika, Aminiyar matar, ta bayyanawa wakilin namu irin zaman da matar take yi da mijin nata, “Dama batun yau ba ta na gaya min abubuwan da yake mata, kodaysushe in ta fada min na kan ce tayi hakuri. Ta tura aka kira ni nazo naga mijin nata yayi mata rauni, to gaskiya ya kamata ace hukuma ta shiga ciki, abi mata hakkinta. A cewar Aminiyar Maryam.

Maryam matar magidancin Muhammad Rabi’u, ta bayyana mana yadda al’amarin ya faru da cewa, “Bayan Magriba ya shigo, na ce ba za ka yi sallah ba ne? Nayi magana ka yi Azahar baka yi ba, ka ce za ka yi, La’asar ba ka yi ba, shi ne ya ce, zan koya masa sallah ne? ya dauke ni da mari ya ce, zan nuna masa musulunci ne? Ya buga min tabarya, na ce zai kashe ni ne? Ya ce, in bashi dukiyar aurensa, ya ce, zai kashe ni yaga mai tsaya min”.

Ko yana shaye-shaye?

“Ya na shaye-shaye, ya na shan wiwi, har ma naga kwaya al’ajihunsa, har ma zai shigo ya fadi, kuma ya na min kashi a wando, nayi masa nasiha, baya salla baya azumi, ya ce zai gyara, ashe bai gyara din ba”.

Dama kin san ya na haka kika aure shi?

Maryam ta kara da cewa, “A’a ban sani ba. ya daki kaina ya hada da gini, ina ihu ya toshe bakina, na samu na kufce ya bini soro ya kama ni ya na jana, shi ne na dauki buta na ce zan je ban daki, na samu na zo soro na yarda butar daga ni sai siket, na fito wajen mutane na ce su taimaka min. Inji Maryam.

Maryam ta ce, ta hakura da auren, ta kuma nemi mahukunta da su taimaka su raba auren nasu, ta kuma yi wa sauran mata nasiha da su rinka gudanar da bincke kafin su yi aure.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending