Connect with us

Labarai

Hukumar Hisba ta fasa giya na makudan milyoyi- Ibni Sina

Published

on

Hukumar Hisba a jihar Kano ta fasa kwalaben giya da kudin ta ya kai kimanin naira milyan dari biyu da hamsin.

Shugaban hukumar Sheikh Harun Ibni Sina ne ya bayyana hakan yau Litinin, a shelkwatar hukumar dake sharada, bayan dawo wa daga sansanin fashen giyar.

Ya na mai cewa, “Shekarar 2004 ne a ka samar da dokar shigowa da giya, raba wa da tace wa, har ma da shan ta, haramun ne. Sannan kuma mataki na biyu kama giyar, mataki na uku neman izini daga kotu domin fashe giyar da aka kama, matakin karshe sahalewar gwamnan jihar Kano domin fasawa”. A cewar Sheikh Harun.

Ibni Sina ya kara da cewa, “Manzon Allah (S.A.W) ya yi tsinuwa a cikin giya, ya tsinewa mutane goma a kan giya, to mutum ya zai yi da wanda annabi ya tsinewa akan giya, saboda haka mu a wurin mu nasara ce, kuma ba yanzu a ka fara ba, hatta zamanin manzon Allah (S.A.W) an yi fashen giya”. Inji Harun Ibni Sina.

Ya kuma ce, “Ba mu gama fashen giyar ba za mu ci gaba da yi, ina godiya da gwamnan jihar Kano, dama sauran jami’an tsaron da su ka bayar da gudunmawa wajen fashen giyar”.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya rawaito cewa, Sheikh Harun IbNI Sina, sun yabawa al’ummar gari akan hadin kan da suke bayarwa domin dakile shigo da giya jihar Kano.

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending