Labarai
Leda uku ta ruwa ta farfado da wata mata da a ka rataye

Ana zargin wasu makwabtan wata mata Marfu’a Mukhtar da rataye ta ranar Asabar din makon da ya gaba ta a unguwar Bubbugaje gidan Jakada dake kamar hukumar Kumbotso.
Al’amarin ya faru ne da misalin karfe goman daren ranar, inda aka yi zargin mutanen guda biyar mata biyu da maza uku sun shiga gidan matar, su ka kuma yi amfani da igiyar guga wajen rataye ta a tagar dakin ta.
Bayan an kai ta asibiti tasha ledan ruwa uku ta farfado farfado, Wakilin mu Abba Isah Muhammad ya zanta da ita tana mai cewa, “Makwabta na ne guda biyu da muke rigima da su, suka zo su ka kwankwasa min kofa su ka ce sun zo mu yi sulhu, ina bude kofa matan biyu suka shigo tare da maza guda uku, matan suka yi dariya suka fita, mijin kwabciyar tawa ne ya bani waya ta ya ce, in kira ‘yan uwana su ceto ni, tunda kome zan yi sai na kira waya, shi ne na kira Abdullahi abokin mijina, sai suka yanki igiyar guga suka nada min a wuya suka rataye min wuya har na fita daga hayyacina. Ni dai abin da nake bukata shi ne mahukunta su bi min hakkina”. A cewar Marfu’a.
Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron dinki ya zanta da mahaifin Marfu’a, Malam Mukhtar Muhammad dake Dorayi Chiranci, inda Ya ce, “Lokacin da abin ya faru wajen karfe goma na dare aka bugo min waya aka ce Marfu’a an rataye ta, gaba daya hankalin mu ya tashi, shi ne na tura wasu su je, saboda matasa sun tafi da makamai, kada su bari yaran su sari kowa, domin kada a bari su dauki doka a hannu, kuma ana zuwa aka ga an rataye ta. Inji Malam Mukhtar.
Kazalika, mijin Marfu’a Sani Isma’il Ya ce, “Na bar cajin waya ta mata ta ta kira wayar ta ba ta samu ba, sai ta kira lambar abokina, sai makwabtan nawa suka afka mata, kuma ko a ofishin ‘yan sanda sun yi barazanar sai sun kashe ni kuma bamu san abin da mu ka yi mu su ba”. A cewar Sani Isma’il.
Shi ma wanda ya ceto Marfu’a, Abudllahi Muhammad Wada, ya magantu da cewa, “Ni ne farkon wanda na fara zuwa gidan nata, da ta kira ni na daga wayar, sai naji an kwace wayar, na kira mijin bai daga ba, ina zuwa na shiga naga an rataye ta, sai na dauke ta a hoto saboda shaida.” Inji Abdullahi Muhammadu.
Wakilin mu Abba Isah Muhammad, ya rawaito cewar, mun yi kokarin jin ta bakin wadanda ake zargi amma basu magantu ba, saboda suna hannun ‘yan sanda, inda kuma Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta wayar hannu ya shaida cewar sun samu labarin faruwar al’amarin amma bai yi martani ba.

Labarai
Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.
Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.
Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.
Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.
A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Labarai
Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.
Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.
“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.
Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Labarai
Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.
Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.
Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.
Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su