Connect with us

Labarai

Leda uku ta ruwa ta farfado da wata mata da a ka rataye

Published

on

Ana zargin wasu makwabtan wata mata Marfu’a Mukhtar da rataye ta ranar Asabar din makon da ya gaba ta a unguwar Bubbugaje gidan Jakada dake kamar hukumar Kumbotso.

Al’amarin ya faru ne da misalin karfe goman daren ranar, inda aka yi zargin mutanen guda biyar mata biyu da maza uku sun shiga gidan matar, su ka kuma yi amfani da igiyar guga wajen rataye ta a tagar dakin ta.

Bayan an kai ta asibiti tasha ledan ruwa uku ta farfado farfado, Wakilin mu Abba Isah Muhammad ya zanta da ita tana mai cewa, “Makwabta na ne guda biyu da muke rigima da su, suka zo su ka kwankwasa min kofa su ka ce sun zo mu yi sulhu, ina bude kofa matan biyu suka shigo tare da maza guda uku, matan suka yi dariya suka fita, mijin kwabciyar tawa  ne ya bani waya ta ya ce, in kira ‘yan uwana su ceto ni, tunda kome zan yi sai na kira waya, shi ne na kira Abdullahi abokin mijina, sai suka yanki igiyar guga suka nada min a wuya suka rataye min wuya har na fita daga hayyacina. Ni dai abin da nake bukata shi ne mahukunta su bi min hakkina”. A cewar Marfu’a.

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron dinki ya zanta da mahaifin Marfu’a, Malam Mukhtar Muhammad dake Dorayi Chiranci, inda Ya ce, “Lokacin da abin ya faru wajen karfe goma na dare aka bugo min waya aka ce Marfu’a an rataye ta, gaba daya hankalin mu ya tashi, shi ne na tura wasu su je, saboda matasa sun tafi da makamai, kada su bari yaran su sari kowa, domin kada a bari su dauki doka a hannu, kuma ana zuwa aka ga an rataye ta. Inji Malam Mukhtar.

Kazalika, mijin Marfu’a Sani Isma’il Ya ce, “Na bar cajin waya ta mata ta ta kira wayar ta ba ta samu ba, sai ta kira lambar abokina, sai makwabtan nawa suka afka mata, kuma ko a ofishin ‘yan sanda sun yi barazanar sai sun kashe ni kuma bamu san abin da mu ka yi mu su ba”. A cewar Sani Isma’il.

Shi ma wanda ya ceto Marfu’a, Abudllahi Muhammad Wada,  ya magantu da cewa, “Ni ne farkon wanda na fara zuwa gidan nata, da ta kira ni na daga wayar, sai naji an kwace wayar, na kira mijin bai daga ba, ina zuwa na shiga naga an rataye ta, sai na dauke ta a hoto saboda shaida.”  Inji Abdullahi Muhammadu.

Wakilin mu Abba Isah Muhammad, ya rawaito cewar, mun yi kokarin jin ta bakin wadanda ake zargi amma basu magantu ba, saboda suna hannun ‘yan sanda, inda kuma Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta wayar hannu ya shaida cewar sun samu labarin faruwar al’amarin amma bai yi martani ba.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending