Connect with us

Labarai

Corona na iya kara kamari har idan a ka gaza bin matakin kiwon lafiya – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta yi gargadin cewa annobar cutar Corona na iya kara Kamari idan har kasashe su ka gaza bin matakan kiwon lafiya, kamar yadda a ka shawarce su su yi.

Shugaban hukumar (WHO) Tedros Adhanom Ghebreyesus yayin wani jawabi kan halin da a ke ciki da hukumar ta saba yi ta fasahar zamani a shalkwatar hukumar da ke Geneva, ya ce har yanzu duniya na fadin tashin yadda za a magance cutar, sai dai alamu sun nuna cewa cutar na kara Kamari.

“Ya ce a kasashe da dama muna ganin yadda ake samun karin kididdigar cutar, amma muna sane da cewa lokaci be kure mana ba kan yadda zamu shawo kan cutar ko da ta yi tsanani sosai, WHO a shirye ta ke ta yi aiki tare da kasashe da ma sauran al’umma ta kuma basu goyon baya domin rage yaduwarta da kuma mace-macen masu kamuwa da ita, bawa yankunan da abun ya shafa goyon baya ta yadda za su kare kansu da sauran jama’a da kuma bawa gwamnatoci goyon baya”.

Amurka ce dai inda cutar ta fi kamari a duniya, yayinda take da sama da mutum miliyan uku na wadanda aka tabbatar sun harbu da Covid-19 inda Brazil ke bi mata da yawan adadin sama da miliyan guda na masu fama da cutar. Ko da yake Dakta Tedros ya ce duk da cewa cutar na kara tsananta, amma wasu kasashen na wasa-re-re da matakan yaki da ita.

 “Ya ce cutar na cigaba da kasancewa barazana, sai dai matakan da wasu gwamnatoci ke dauka da ma sauran al’umma ko kadan baya nuna alamun yaki da cutar, idan har gwamnatoci suka gaza fahimtar da al’ummominsu da inganta matakan kariya, ta yadda za a kare rayuka, idan har al’umma ba zasu bi dokokin yaki da cutar ba, musamman bayar da tazara, shakka babu wannan annoba zata bi hanyar da zai sa ta sake yin tsanani ne, na sani cewa shugabanni da dama yanzu haka sun shiga tsaka mai wuya sakamakon annobar, amma muna bukatar amfani da abin da muke da shi ta yadda zamu shawo kan ta”.

Sama da mutum miliyan 13 ne aka tabbata sun harbu da Coronavirus a fadin duniya, inda ta yi ajalin kusan mutum 572,000.

A cewar rahoton kididdigar da jami’ar Johns Hopkins ta kasar Amurka ta fitar, kasashen Brazil, Mexico, Burtaniya, Amurka da kuma Italiya ne suke da mafi yawa na adadin mutanen da cutar ta yi ajalin su.

Labarai

Abin takaici ne yadda ake fuskantar ƙarancin ruwan Sha a sassan jahar mu – Gwamnan Kano.

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nuna rashin jin daɗin sa bisa yadda ake samun ƙarancin Ruwan Sha, a wasu daga cikin sassa jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga manema labarai, a lokacin a ya kai ziyarar gani da ido, matatar Ruwa da ke Tamburawa a yammacin yau Juma’a, a ƙokarin sa na na gyara ɓangaren ruwan a cikin garin Kano.

Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kuma sha alwashin tabbatar wa al’umma cewar, gwamnatin sa za ta yi aiki ba dare ba rana domin tabbatar da isasshen ruwan Sha ga al’ummar jihar Kano.

Gwamnan ya ƙara da ce a lokacin da suka zo ba sufi mako biyu ba suka samar da ingantaccen Ruwan sha, wanda ya rinƙa shiga cikin lunguna da Sako na sassan jihar.

Continue Reading

Labarai

Ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da sayar da Burtalai a wasu garuruwan ta

Published

on

Biyo bayan kokawar da wasu Fulani Makiyaya suka yi kan yadda wasu suka gididdiba burtalai yayin da aka siyarwa Manoma, a garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, yanzu haka ƙaramar hukumar Tofa ta dakatar da taɓawa, ko kuma sayar da dukkanin Burtalan kiwon shanun ba tare da ɓata lokaci ba.

Shugaban riƙon ƙaramar hukumar ta Tofa Abubakar Sulaiman Mai Rogo, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a ranar Alhamis.

Mai Rogo, ya kuma ce ƙaramar hukumar ba ta da hannu a kan taɓa dukkan guraren, a dan haka sun dakatar da dukkanin yunƙurin taɓa Burtalan har sai shugabanni na kwamitin ƙasa sun kammala bincike wanda yanzu haka ake ci gaba da yi.

Da yake nuna jin daɗin sa kan matakin dakatarwar, amadadin Fulanin garuruwan, shugaban ƙingiyar Funali Makiyaya ta Gan Allah, Ahmad Shehu Gajida, yabawa gwamnatin jihar Kano, da kuma ƙaramar hukumar ta Tofa ya yi, bisa karɓar koken su da suka akai.

A baya-bayan nan ne dai a zantawar Dala FM Kano, da wasu Funalani Makiyaya mazauna garuruwan Yanoko da Gajida da kuma Dindere, suka koka kan yadda aka gididdiba burtalan a yankunan nasu aka siyarwa manema, lamarin da suka ce ka iya sawa su rasa guraren da za suyi kiwon shanun su wanda hakan babbar barazana ce a gare su.

Continue Reading

Labarai

Ku guji zubar da Shara barkatai a muhallan ku – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta gargadi al’umma da su kaucewa zubar da shara a wuraren da ba’a tanade su ba, domin kaucewa yawaitar samun cutuka a tsakanin al’umma, duba da yadda ake ci gaba da tunkarar lokacin Damuna.

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar Kano Ambasada Ahmadu Haruna Zago, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake sanya ido kan aikin kwashe sharar da ke unguwar Zango hauran gadagi bayan Festival.

Ya ce duba da yadda Damuna ke ci gaba da tunkarowa, akwai bukatar al’umma su fahimci cewa zubar da shara barkatai ka iya haifar da cututtuka daban-daban ga iyalan su, musamman ma kasancewar sharar da ke unguwar ta Zango bayan Festival, tana tsakiyar gidajen al’umma ne da kasuwa da kuma makaranta.

Nazifi Mohammed Usman mai Duniya, da Mohammed Ibrahim wato Halifa mai Gas mazauna unguwar ta Zango ne, sun ce tarin sharar a cikin unguwar su babban ƙalubale ne a gare su, domin kuwa taruwar da tayi har ta kan shiga cikin makarantar yankin su.

Shugaban hukumar kwashe sharar Ahmadu Zago, ya kuma sha alwashin yin duk mai yiwuwa wajen tsafta ce birnin Kano, wajen kwashe shara daga kowane yankin, domin gudun faruwar ambaliyar ruwa sanadin sharar da ka toshe magunan ruwa a jihar Kano.

Continue Reading

Trending