Connect with us

Lafiya

Wata mata ta kubuta da kyar a wurin mai Adaidaita sahu

Published

on

Ana zargin wata mata da ta shiga baburin adaidaita sahu mai adaidaita sahun ya so guduwa da ita inda kuma ta kubuta dakyar.

A zantawar gidan rediyon Dala da wannan mata ta bayyana yadda almarin ya faru da ita.

Ta ce, “Mun hau adaidaita sahu daga Sabo titi Gidan Karkara za’a kai mu unguwar Kuntau, sai da muka zo Junction din da za’a shiga Jambulo sai na ce malam ka bi ta nan, sai ya ce shi ba zai bi ba akwai sakon da zai karba, mu na cikin tafiya sai ya kai mu can wani lungu a can cikin Rijiyar Zaki, ya ce wai kwan lantarki zai siya, bai fada ba sai da mu ka zo cikin wani layi a Rijiyar Zaki, layin da ban ma san sunan sa ba”.

Ta kara da cewa, “Sai na ce malam duk ga shaguna nan ka siya, sai ya ce, babu inda zai samu sai a can, da ya shigar da mu wani layi akwai wani kanti, ya ce ga kantin nan anan zai samu gulob din, kuma ya na ajiye mu layin tsit babu kowa, kuma bai shiga kantin ba sai ya mike cikin wani layi mai duhu, sai naga ya dauko waya, ya na waya daga nesa ina hango shi, sai na gan shi tare da wasu mutane guda biyu, sai Allah ya bani nasara ni da yara na muka fito da gudu, da kyar mu ka sha mu ka fito bakin titi, mu ka samu wata motar muka hau”. Inji matar

A nasa bangaren, mijin wannan mata, Adam Bashir Yakubu, shima yayi Karin bayani a kan yadda al’amari ya faru, “Akwai iyalina da su ka hau adaidaita sahu zai kawo su Kuntau, su na tafiya ba fitila a daidaita sahun, sun zo Kabuga ya ce zai biya Rjiyar Zaki ya sayi kwan lantarki. Ina so jama’a su kula iyali na da kyar su ka sha, idan adaidaita sahu babu fitila kada su hau”. A cewar Adam Bashir

Wakilin mu Abubakar Sabo ya rawaito cewa, Adam Bashir ya kuma yi kira ga jamai’an tsaro a kan su tashi tsaye wajen al’amarin tafiya da adaidaita sahu babu fitila, domin miyagu sun fara amfani da hakan domin cimma burin su.

Lafiya

Ku rinƙa ziyartar Asibiti ana muku gwaje-gwajen fitsari da Jini domin sanin halin da ƙodar ku take ciki – Likita

Published

on

An shawarci al’umma da su rinƙa ziyartar Asibiti akai akai wajen duba lafiyar su, ta hanyar yin gwaje-gwajen fitsari da jini domin sanin halin da kodar su ke ciki.

Dakta Muhajid Sunusi Rabi’u ne ya bayyyana hakan yayin ganawarsa da Dala FM, lokacin da suke aikin gwaje-gwajen fitsari da jini, kyauta a ɗaya daga cikin makarantu masu zaman kan su a nan Kano.

Dakta Mujaheed ya kuma ce sun gudanar da aikin ne a wani ɓangare na bikin ranar ƙoda ta Duniya, wadda aka ware duk ranar Alhamis ta mako na biyu na kowanne watan Maris domin gudanar da bikin ranar.

Continue Reading

Lafiya

Za’a yiwa kusan yara miliyan 3 rigakafin cutar shan Inna a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace kusan Yara miliyan 3 za’ayiwa rigakafin cutar shan inna a kananan hukumomin jihar nan 44, duba da samun ɓurɓushinta da kaso 65, a jihar ta Kano.

Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dakta Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da rigakafin cutar shan innar a yau Alhamis, wanda za’a kwashe kwanaki 4 ana gudanarwa a Kano.

Dakta Abubakar Labaran ya ce duba da shigowar zafin akwai buƙatar al’umma su kula da alamomin cutar sankarau, duk da gwamnati ta yi shirin bayar da agajin gaggawa, kamar yadda tashar Dala FM Kano ta rawaito.

Ma’aikatar lafiyar ta jihar Kano dai ta ce za’a ci gaba da gudanar da sauran rigafin, domin bai wa yaran jihar Kano kariya daga cututtuka masu yaɗuwa.

Continue Reading

Lafiya

Dokar tilasta gwajin lafiya kafin aure ta tsallake karatu na biyu a majalisar dokokin Kano

Published

on

Rahotanni na bayyana cewar majalisar dokokin jihar Kano, ta yi karatu na biyu a kan kudirin dokar tilasta wa masu niyyar yin aure yin gwajin cutar kanjamau, da na cutar hanta da kuma duba kwayoyin jini wato Sikila, gabanin daura aure.

Ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Takai, Hon.Musa Ali Kachako, shin wanda ya kawo kudirin dokar, ya bayyana cewa, jihar Kano na fama da matsalolin lafiya daban-daban da suka hada da cutar kanjamau saboda mutane kan yi aure ba tare da an duba lafiyarsu ba, hakan ne ma ya sa ya kai ƙudirin.

Kachako, ya ce, ƙudirin dokar idan har aka amince da shi, zai ceci rayuka da dama tare da dakile yaɗuwar cututtuka masu barazana ga rayuwar al’umma, kamar yadda jaridar Kadaura24 ta rawaito.

Da yake nuna goyon bayansa kan ƙudirin Ɗan majalisa Hon. Aminu Sa’ad, mamba mai wakiltar mazabar Ungogo, ya ce, jihohin Jigawa, Katsina da Kaduna sun zartar da irin wannan kudiri domin magance kalubalen kiwon lafiya da suke fuskanta.

Ya ce tilas ne Kano da ke da yawan al’umma a kasar nan ta zartar da kudirin dokar, domin kare lafiyar ‘yan jiharta ta hanyar samar da gwaje-gwaje kafin aure domin dakile yaduwar cututtuka, kamar cutar hanta, da sauran cututtuka.

Continue Reading

Trending