Connect with us

Labarai

Mun yi kotun tafi da gidan ka a kan kin saka safar baki da hanci – Ganduje

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta fito da kotun tafi da gidan ka da za ta rinka hukunta wadanda basa bin dokar sanya safar baki da hanci domin kariya daga yaduwar cutar Corona.

Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi lokacin da ya ke sake kaddamar da rarraba safar baki da hancin a fadar gwamnatin jihar Kano.

Ya ce, “Za mu hada kai da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da mutane na bin dokar saka safar baki da hanci”. Inji Gwamnan Kano

A nasa jawabin, shugaban kwamitin karta kwana kan cutar Corona kuma mataimakin gwamnan jihar Kano Nasir Yusif Gawuna, Ya ce “Nan bada dade wa ba in Allah ya yarda kamar yadda mai girma gwamna ya fada za’a yi maganin wannan cuta, wannan safa ta hanci da baki, idan mutane ba su manta ba kananan hukumomi sun bayar da aikin raba ta na milyan guda, itama gwamnatin Kano ta bayar da na milyan guda, a yanzu kuma ta kumae bayar da aikin na milyan guda, idan an yi lissafi, an yi na milyan uku kenan”. A cewar mataikin Gwamna

Da yake jawabi sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce, “Yanzu gwamnati da jami’an su an samu gangara a na samun sauki. Mu na kira da jama’a su ka ci gaba da bin dokokin gwannati, ta hanyar saka safa da wanke hannu da kuma bin shawarar likitoci. Wadanda mu ka rasa a dalilin wannan cuta Allah ya jikan su, wadanda su ka kamu Allah ya ba su lafiya. Mutane su daure wajen kiyaye kai a lokacin sallah, tare da hakura da yawace-yawace, domin Kare kai daga yaduwar cutar Corona”. Inji Sarkin Kano

Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta ruwaito cewa, Gwamna Dr Abdullahi Ganduje ya kuma ce, al’umma za su je sallar idi ranar sallah da kuma sallar juma’a a don haka ne ya bukaci mutane da yin addu’ar magance cutar Corona.

Labarai

Mahukunta ku kawo mana ɗauki a masallacin garin mu – Mazauna garin Ɗan-Dalama

Published

on

Al’ummar garin Ɗan-Dalama da ke ƙaramar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano, sun koka tare da neman ɗaukin mahukunta kan yadda katangar masallacin Juma’a na garin ta lalace, lamarin da hakan ke barazanar faɗuwar katangar.

Shugaban kwamitin masallacin juma’ar na garin Ɗan Dalama, Mallam Muhammad Mai Nama, ne ya magantu kan al’amarin, inda ya kuma yi kira ga al’umma ciki har da Attajirin ɗan kasuwar nan Alhaji Alhassan Aminu Ɗan Tata, da su kawo musu ɗauki domin gyara katangar masallacin na Ɗan Dalama, bisa yadda take neman faɗuwa.

Ya kuma ƙara da cewa ba iya katangar ce ke barazanar faɗuwar ba, haka ma cikin masallacin ba a cewa komai, duk kuwa da ƴan kwamitin sun yi bakin ƙokarin su, amma dai kawo yanzu akwai gyare-gyaren da ya ke buƙata.

Continue Reading

Labarai

Ba za’a iya wadata mutane da Fetur ba idan gwamnati ba ta sa hannu ba – Bashir Ɗan Mallam

Published

on

Yayin da ake ci gaba da fuskantar tsadar man fetur a ƙasar nan, shugaban kungiyar Dillalan Man fetur da Iskar Gas, ta ƙasa Bashir Ahmad Ɗan malam, ya ce koda kuwa matatar Mai ta Dangote za ta yi ƙarfi ka’in da na’in, ba lallai ne a samu saukin Man fetur ba a ƙasa, matuƙar gwamnatin tarayya bata sa hannu ba.

Bashir Ɗan Malam ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da gidan rediyon Dala FM, da safiyar yau Juma’ar.

Ɗan Mallam ya kuma ce sakamakon yadda gwamnati take taimakawa a fagen shan man, hakan yasa idan har bata sanya hannu ba za’a rinƙa shan wahala wajen samun man fetur ɗin a ƙasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’umma ke ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsadar man fetur, lamarin da ya sa ake siyar da kowacce lita sama da Naira 800 a jihar Kano, inda ake ci gaba da fuskantar manyan layuka a gidajen man da dama.

Continue Reading

Labarai

Zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ƴan Jarida – Hukumar Zaɓe ta Kano

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSEC, ta sha alwashin aiki kafaɗa-kafaɗa da ma’aikatan Jarida, musamman ma da zaɓen ƙananan hukumomin jihar nan 44 da ke tafe.

Sabon shugaban hukumar Farfesa Sani Lawan Manumfashi, ne ya bayyana hakan, yayin ziyarar da tawagar ƙuniyar matasan ƴan Jarida, ta Kano Youth Journalist Forum, suka kai masa a ofishin sa yau Alhamis, yayin da ya shafe kwanaki huɗu da kama aiki.

Ya kuma ce, za su yi aiki da ma’aikatan Jarida musamman ma yayin gudanar da ayyukan zaɓen ƙananan hukumomin Kano 44, da ke tafe, domin wayar da kan al’umma da ma samun nasara yayin zaɓen da ma bayan sa.

Farfesa Manumfashi, ya kuma ƙar da cewa, akwai buƙatar kowa ya bayar da tasa gudummawar a harkar zaɓe, domin kuwa yanzu haka suna ci gaba da aiki wajen shirya zaɓen ƙananan hukumomin.

Da yake nasa jawabin shugaban ƙungiyar matasa ƴan Jaridar ta jihar Kano Musa Zangina Adam, ya ce sun kai ziyarar ne, domin su ƙulla alaƙar aiki a tsakanin su da hukumar, bisa yadda kowanne ɓangare yake buƙatar juna, tare kuma da bayar da gudunmawar da ya kamata.

Zangina, ya kuma ce a shirye ƙungiyar su take wajen ci gaba da bibiyar al’amuran da suka shafi al’umma, tare da nusar da mahukunta dan ganin an wadata su da kayayyakin more rayuwa.

Continue Reading

Trending