Connect with us

Labarai

Kisan wuta: Magidanci ya kai karar tsohon mijin matar sa kotu

Published

on

A na zargin wani mutum mai suna Usman Ali dake unguwar Dabai a jihar Kano da bibiyar tsohuwar matar sa da ya sake ta, bayan ta tare a gidan sabon mijin ta, har ma kuma ake zargin ya saya mata waya yana kiran ta suna haduwa a wani wajen daban.

Tun da fari dai an gabatar da Usman Ali a kotun shari’ar musulunci dake Post Office, daga bisani alkalin ya bukaci a mayar da shi wajen ‘yan sanda domin su fadada bincike, bayan kuma sun yi binciken aka mika takardar tuhumar harabar rukunin kotuna dake Sakatariyar Audu Bako domin sanin kotun da za’a fara sauararen karar.

A zantawar gidan rediyon Dala da sabon mijin matar mai suna, Malam Musbahu Nasir a ranar Talata ya bayyana yadda al’amarin ya faru.

“Duk bibiyar da ake yiwa mata ta tsawon shekaru biyu da rabi, Allah ne da ikon sa yake kare ta, shekarar da ta gabata har fitar da ita ya yi daga gida na ya bata kudin mota ta tafi garin ‘yan uwan mahaifiyar ta domin su zo a raba aure na da ita, daga baya iyayenta da na aure ta a hannunsu su ka gane gaskiyar al’amarin su ka dawo da ita su ka ga ma ba’a hayyacinta take ba”.

Ya kuma ce, “So yake yi in sake ta ya sake aure ta, saboda shi ya cutar da ita a lokacin da su ka yi aure, ni kuma na gane haka, amma bai daina ba ya ci gaba da bibiyar ta, har ‘ya’yan ta ya aiko da magani ta rinka sha shafawa, sai daga baya ta gane, a shekarar nan ma sai da ya kuma fitar da ita daga gidan ta bar jihar ta tafi wajen wan mahaifiyar ta, ya dawo da ita gida, amma a karshe bayan an yi addu’a da kanta ta bukaci ganina ta kuma ce za ta bayyana min duk abubuwan da su ka faru, ta nuna min waya ta ce tafi wata uku da ita muke waya da shi”.

Ya kara da cewa, “To ina gayawa duniya yanzu na fara son mata ta, kuma da ta zo gidana ta samu kulawa, ba zagi ba wulakanci, bata shekara ba ta canja, ai bai iya zama da mace ba, mace ‘yar rarrashi ce… Ni bukata ta na yarda shari’a za ta yi adalci a kan abun da yayi min, domin ina da shaidu”. A cewar Malam Musbahu Nasir

Wakilin mu Ibrahim Abdullahi Soron dinki ya rawaito cewar, ya tuntubi Usman Ali wanda ake zargi, amma ya ce baya tare da lauyan sa, saboda haka  ba zai iya cewa komai ba.

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.

Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.

Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.

Continue Reading

Trending