Connect with us

Wasanni

Gwarzon dan wasa: Arnold ya lashe kyautar bayan ya doke ‘yan wasan Man United 3

Published

on

Dan wasan gefefn bayan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Trent Alexander-Arnold ya zama gwarzon dan wasa ajin matasa na kasar Ingila bayan da ya doke ‘yan wasan Manchester United.

Arnodl, mai shekaru 21 dan kasar Ingila ya samu nasara ne bayan da magoya baya su ka zabe shi a matsayin gwarzon dan wasan gasar Firimiya na wannan kakar.

Dan wasan ya samu nasarar zura kwallayen da su ka tallafa Liverpool ta lashe gasar Firmiyar kasar Ingila a bana wanda ya kawo karshen shekaru 30 da kungiyar sa ta yi ba ta dauki gasar ba.

Kwallaye 12 da dan wasan Alexander-Arnold, ya zura su ne su ka ciciba kungiyar sa wajen bas hi damar lashe kyautar inda ya doke ‘yan wasan Manchester United ciki akwai, Mason Greenwood da Anthony Martial da kuma Marcus Rashford.

Cikin zaben su ma sauran ‘yan wasa ciki akwai na Chelsea Christian Pulisic da kuma Mason Mount tare da dan wasan Aston Villa, Jack Grealish da kuma na Sheffield United, Dean Henderson.

Kyautar dai ‘yan wasa ma su hazaka wadanda shekaru ya kai kasa da 23 wanda magoya bayan gasar Firimiya ke fitar da gwani a cikin su a duk shekara.

Alexander-Arnold ko a shekarar bara dan wasan sai da ya lashe kyautar bayan da ya takwarorin sa Jordan Henderson da Sadio Mane da kuma Kevin De Bruyne da Jamie Vardy tare da Nick Pope da Danny Ings.

 

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending