Connect with us

Wasanni

Manchester City za ta yi mutumin mutumi na David Silver

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, ta ce ta na shirye-shiryen yin mutumin mutumi na Davida Silver bayan da ya shafe shekaru 10 ya na fafatawa a kungiyar.

A shekarar 2010 ne dai dan wasan tsakiyar ya koma Manchester City daga Valaencia, inda ya buga wasanni 436 ya lashe kofi har guda 14 a kungiyar.

Dan wasan mai shekaru 34, ya sanar da karshen wasan sa a ranar Asabar din da ta gabata, bayan da Lyon ta fitar da su a gasar kofin Champions League.

Mai kungiyar, Khaldoon Al Mubarak ya ce“David ya guna mana Manchester City, kuma ya zama jagora a kungiyar, ya hada kan kowa, yin mutumin mutumin sa zai sa mu rinka tunawa da shi a ko da yaushe”.

A shekarar 2021 ne za a yi mutumin mutumin dan wasan tare da na Vicent Kompany.

Silva ya buga wasanni 309 ya zura kwallaye 60, sannan ya lashe gasar Firimiya a shekarar 2012 da 2014 da 2018 da kuma 2019.

Ya buga wasanni 57 a sauran gasar cin kofi, inda ya lashe gasar FA biyu da League Cup biyar da kuma Community Shields uku.

Ya kuma kafa tarihi, inda ya zama dan wasa da ya fi kowa taka leda a kungiyar Manchester City a nahiyar turai, inda ya buga wasanni 70 a Champions League a iya tsawon shekaru 10.

 

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending