Connect with us

Wasanni

Ballon d’Or: Manuel Neuer ya fi cancanta a kan Lewandowski – Mai horas da kasar Jamus

Published

on

Mai horas da kasar Jamus, Joachim Low ya ce ya yarda mai tsaron ragar Bayern Munich, Manuel Neuer ya fi cancantar lashe kyautar gwarzon kwallon kafa na duniya a kan dan wasan gaban kungiyar, Robert Lewandowski.

Wannan batun na zuwa ne a lokacin da mai tsaron ragar Manuel Neuer ya tallafawa kungiyar sa ta Bayern Munich ta lashe kofi Uku a jere a kakar da a ka karkare a bana.

Ya ce”Manu ya yi kokari sosai a kakar 2019-20, kuma dan wasa ne mai matukar bada mamaki, b azan iya cewa komai a kan Lewandowski ba, saboda shi ma dan wasa ne na zahiri wajen zura kwallaye, amma ni a karan kai na, na fi gamsuwa da Manuel Neuer ya lashe kyautar zakaran kwallon kafa na duniya, saboda ya taka rawar gani sosai wajen lashe gasar cin kofin zakarun kungiyoyin nahiyar turai, saboda lokacin wasan Lyon da PSG akwai kwallayen da za a ci a raga ya tare su, kuma idan ka duba wasan wani z aka ga ko a ci kungiyar sa ko kuma ta yi kunnen doki 1-1, kokarin sa a Champions League zai iya bashi damar lashe kyautar Ballon d’Or na shekarar 2020”. Inji Low.

Kyautar dai a bana tun a watan Yuni ne mahukuntan kasar Faransa du ka sanar da dage bayar da kyautar da a ka shirya bayar wa a watan Disamba na shekarar 2020, sakamaon cutar Corona.

 

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending