Connect with us

Labarai

NNPC: Cire tallafin mai zai sanya a daina cuwa-cuwa – Malam Mele Kyari

Published

on

Shugaban kamfanin mai na kasa NNPC Malam Mele Kolo Kyari ya ce, wasu daidaikun mutane ne kawai ke amfana da tallafin man fetur da gwamnati ta ke bayarwa, wanda bayar da tallafin ke janyo duk matsalolin da ke faruwa.

Malam Mele Kolo Kyari, ya bayyana hakan ne a zantawar sa da gidan rediyon Dala.

Ya ce, “Daga shekarar 2006 zuwa yanzu an kashe kudi sun wuce  Naira Tiriliyan goma sha hudu, kuma tallafin ba za ka nuna cewa ga abin da a ka yi da shi ba”.

Ya kuma ce, “Cire tallafin ya sanya za a daina yin cuwa-cuwa, kudin za su yi wa hukuma da al’ummar Najeriya amfani, kuma babu zancen sayar da matatar mai, yanzu batu a ke yi na samo mutanen da za su zuba hannun jari ne a ciki”. A cewar Malam Mele Kolo Kyari

Wakilinmu Abba Mika’ilu Dandami ya rawaito cewar, Malam Mele Kolo Kyari ya kuma kara da cewa, idan a ka kammala aikin shimfida bututun iskar gas daga Abekuta zuwa Kaduna ya wuce jihar Kano, masana’antun da a ka rufe duk za su tashi, kuma za a samu sababbin masana’antu, kuma za a samu wadatuwar wutar lantarki, kuma za a samu ayyukan yi.

 

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending