Connect with us

Labarai

Jam’iyyar PDP ta dakatar da ‘dan takarar gwamnan Kano

Published

on

Jam’iyyar PDP ta dakatar da tsohon ɗan takarar gwamnan Kano Ibrahim Al’amin Little na tsawon wata guda.

Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar PDP na ƙaramar hukumar Nassarawa Sulaiman Mustapha Mainasara ne ya tabbatar da hakan a tattaunawar sa da Dala FM.

A cewar sa, shugabancin mazaɓar Tudunwada ne ya aike musu da takardar dakatarwar bisa zarginsa da aikata laifukan da suka saɓa da kundin tsarin mulkin jam’iyya.

Ana zargin Little da tsame kansa daga al’amuran jam’iyya sannan ya kai jam’iyyar ƙara kotu, ba tare da yin ƙorafi ga jam’iyya ba, sannan ana zarginsa da yiwa jam’iyyar zagon ƙasa a cewar Mainasara.

Har kawo lokacin haɗa wannan rahoto Alhaji Al’amin Little bai ce komai ba a kai.

Wannan rikici na cikin gida, abu ne da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a Kano, ko a makon da ya gabata ma, tsagin Ambasada Aminu Wali ya sanar da korar tsohon gwamna Kwankwaso daga jam’iyyar.

Sai dai tsagin Kwankwaso ya yi watsi da korar da aka yi masa.

Yayin da ake rikicin shugabanci tsakanin ɓangarorin biyu, uwar jam’iyyar ta ƙasa ta ce tsagin Kwankwaso su ne halastattun shugabannin jam’iyyar.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending