Connect with us

Wasanni

Za mu warware matsalar tsakanin gidan kallo na da magoya bayan Arsenal – Hamisu Abubakar

Published

on

Magoya bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal a jihar Kano, ta umarci magoya bayan ƙungiyar da su ƙauracewa shiga gidan kallon ƙwallon ƙafa na unguwar Makasa da ke Ɗan Rimi a ƙaramar hukumar Gwale.
Shugaban ƙungiyar na jihar, Ibrahim London Boy ne ya tabbatar da hakan ta bakin babban sakataren ƙungiyar, Aminu So Far Mai Arsenal.

Shugabancin ya yanke wannan hukuncin ne, sakamakon zargin cin zarafin magoya bayan Arsenal da a ka yi a gidan Kallon na yin ɓangaranci.


Sanarwar ta ƙara da cewa, ƙungiyar su ta shigar da ƙara zuwa shugabancin da ke jihar Legas, wanda hakan ya ba su damar shigar da ƙorafin su zuwa ƙungiyar da ta ke kula da gidajen kallon ƙwallon ƙafa a jihar, amma kawo yanzu ba su ji amsa ba, wanda shugabancin magoya bayan ƙungiyar ya yi kira ga ƴaƴan ta da su ƙauracewa shiga gidan kallon har sai sun ji amsa a nan gaba.


Mun kuma tuntuɓi mai gidan kallon, Hamisu Abubakar, ya ce za su yi zama da shugabancin kungiyar ta Arsenal nan da mako mai zuwa, domin warware matsalar, kamar yadda su ka cimma matsaya tsakanin shugabancin da kuma shi kan sa mai gidan kallon.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending