Connect with us

Labarai

Mai shirin zama Ango: Matashi ya nemi kotu ta kwato masa da N708,500 da ya kashewa budurwa

Published

on

Babbar kotun shari’ar musulinci mai zaman ta a Rijiyar Lemo karkashin mai shari’a, Aliyu Muhammad Kani, ta sanya ranar 3 ga watan gobe, domin ci gaba da sauraron wata kara wanda wani mutum mai suna, Muhammad Sani ya shigar ya na karar, Malam Surajo Ya’u da mutum daya.

Mai karar ta bakin lauyansa, Barista Nuhu Jafar, ya nemi taimakon Shari’a da ta sanya wanda a ke kara da mutum daya su dawo da wasu kudade da su ka yi alkawarin dawo da su tun a shekarar 2020.

Kunshin da’awar ya bayyana cewar, mai kara Muhammad Sani, ya nemi auren ‘yar gidan wanda a ke kara, kuma magana ta yi nisa daga karshe a ka ce an fasa bashi auren ta. Domin haka ya nemi a dawo masa da wa su kayayyaki cikin abinda ya nemi a dawo masa da su ka hadar da Leshi ruwan hoda mai kimar Naira Dubu 35, sai wani Leshin mai kimar Dubu 35, shi ma ruwan Lemo da kuma wani Leshin wanda ba a fadi kalar sa ba, mai kimar Dubu 25 da wayar salula ta Naira Dubu 50 da hodar shafawa ta Naira 25 da kuma zunzurutun kudi Dubu 397, sai kuma rigar sanyi wadda a ka saya mata ta Dala 281, wadda in a ka canza kudin sun kai Naira Dubu Dari da Arba’in da Biyar. Jimlatan abin da mai kara ya ke nema a biya shi Naira Dubu Dari Bakwai da Dubu Takwas da Dari Biyar (708,500).

Bayan kammala da’awa, lauyan wanda a ke kara Barista Ya’u Abdullahi Umar, ya yi suka a kan cewar da’war ma sam ba ta tsaya ba, domin mai kara ya gaza bayyanawa kotun wannan kayan da kudin ko wane dalili ne ya sanya a ka bayyar da su.

Mai shari’a Aliyu Muhammad Kani, a cikin kwarya-kwaryar hukunci da ya yi ya bayyana cewar, da’awar ma su kara ta tsaya kuma kotu za ta yi mu su shari’a. Daga nan lauyan wadanda a ka yi kara ya nemi a sa masu wata rana, domin yin martani a kan da’awa, sun kuma musanta dukkanin da’awar da a ka gabatar gaban kotu.

Wakilinmu, Yusuf Nadabo Ismail, ya rawaito cewar, lauyan wanda a ka yi kara ya kuma roki kotun da ta ba su damar zaunawa a waje, domin sasantawa kafin waccan rana ta 3 ga watan Disambar 2021

Labarai

Kisan gillar Edo: A gaggauta nemawa mutanen da aka kashe haƙƙin su, ko mu ɗauki Mataki bisa doka – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Rights Network, ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta Kano da kuma ta jihar Edo, da gaggauta neman haƙƙin Mafarautan nan ƴan asalin jihar Kano waɗanda aka yi wa kisan gilla a garin Uromi na jihar Edo.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Gambo Madaki shi ne ya bayyana wa tashar Dala FM Kano, hakan a ranar Litinin, lokacin da yake tsokaci kan kisan sama da Mafarauta 16 a jihar Edo, waɗanda suka taho daga jihar Ribas za su dawo gida Kano.

Ya ce baya ga ɗaukar matakin lalubo waɗanda suka aikata rashin imanin, akwai buƙatar a ɗauki mummunan mataki akan su don daƙile afkuwar irin hakan a gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ɓatabgari ne su ka damke wadanda abin ya shafa a Uromi da ke karamar hukumar Esan ta Arewa maso Gabas ta Jihar Edo, inda su ka ga bindigogin farauta, sai kawai su ka yanke cewa ai masu garkuwa da mutane ne, inda suka kona su da ransu a ranar Alhamis.

Lamarin dai ya jawo cece-ku-ce, inda ‘yan Najeriya da dama ke zargin gwamnati da gazawa wajen dakile irin wannan ɗaukar doka a hannu.

A cewar Gambo Madaki, baya ga batun kafa kwamiti da gwamnatin Kano ta yi akan wannan batun, ya kamata gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙara bibiyar lamarin da kan sa, don ganin an ɗauki matakin da ya dace akan kisan gillar ko kuma su ɗauki mataki bisa doka.



Continue Reading

Labarai

Mun baza jami’an mu lungu da saƙo don samar da tsaro yayin bikin Sallah a Kano – Anty Snaching Phone

Published

on

Rundunar tsaron nan da ke yaƙi da faɗan Daba da ƙwacen Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye, ta Anty Snaching Phone, ta ce ta baza jami’an ta kusan dubu ɗaya da za su shiga lungu da saƙo na jihar nan, domin samar da tsaro a yayin bukukuwan ƙaramar Sallah.

Kwamandan rundunar a nan Kano Inuwa Salisu Sharaɗa ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da Freedom Radio, ya kuma ce jami’an su za su yi duk mai yiyuwa wajen daƙile ayyukan ɓata garin da ke shirin tayar da hankalin al’umma yayin bikin sallar.

“Daga cikin jami’an mu da za su samar da tsaron akwai na cikin kayan mu da kuma na farin kaya, kuma sun fara bazama guraren da mu ka tura su tun cikin kin daren Asabar ɗin nan kuma za su yi aiki cikin ƙwarewa kamar yadda suka samu horo, “in ji Inuwa”.

Sharaɗa, ya kuma ce hakan na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar Kano ƙarkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa kulawar shugaban kwamitin karta-kwana da ke yaƙi da miyagun ɗabi’u da gwamnan ya kafa ƙarkashin Dakta Yusuf Ƙofar Mata.

Wannan dai na zuwa ne yayin da za’a gudanar da sallar Idi, ta ƙaramar Sallah a ranar Lahadin nan a Najeriya, da Jamhuriyyar Nijar da ƙasar Saudiyya, da ma wasu ƙasashen Duniya.



Continue Reading

Labarai

Za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 – Masani

Published

on

Wani masanin ilmin Taurari da ke jihar Kano a arewacin Najeriya, Mallam Nasir Falaki Al-Kanawi, ya ce za a cika Azumin Ramadan na shekarar 1446 guda 30 saboda watan Shawwal ba zai ganu ba a ranar Asabar, don da ƙarfe 11:58 na safe za a haifi jinjirin watan kuma zai faɗi 06:48 na Yamma.

Mallam Nasiru Alfaki Al-Kanawi ya bayyana hakan ne a wani taƙaitaccen jawabi da ya yi wa gidan rediyon Dala FM Kano a ranar Juma’a 28 ga watan Maris ɗin shekarar 2025.

Alfalaki ya kuma ce watan zai faɗi ne da ƙarfe 6:48 na yamma mintuna kasa da 10 kenan bayan faduwar Rana, kasancewar ranar ƙarfe 6:37 na yamma za ta fadi.

Ya ci gaba da cewa to wannan dalilin ne zai sa watan ba zai ganu ba, ko da kuwa da Na’ura ne kasancewar bai samu wadataccen hasken da zai ɗosana daga ranar ba, wanda aƙalla yana buƙatar awanni 13 zuwa 16 daga haifeshi kafin ace an iya ganinsa, Allah shi ne mafi sani Mai iko akan komai.



Continue Reading

Trending