Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Kaso 35 na kasashen Turai za su iya rasa iskar Gas daga Rasha

Published

on

Kaso 35 na wasu kasashen nahiyar Turai za su iya fadawa kangin rashin iskar Gas, muddin har idan Rasha ta katse hanyoyin iskar Gas din da take tunkudawa yankunan.

Kmfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, rigingimun da ke kokarin aukuwa tsakanin Amurka da Rasha a kan iyakar Ukraine na tura sojoji dubu 10 yankin wanda ya sanya Amurka ke kara matasa Rasha kan ta janye sojojin ta.

Shugaban Rasha, Vladimir Putin ya yanke shawarar yin amfani da abin da manazarta sukan kira “makamin iskar gas” na Moscow, na tozarta zai yi tasiri ga wasu kasashen Tarayyar Turai fiye da sauran.

Bambance-bambancen tasirin tasiri ya samo asali ne daga yadda aka tsara kasuwannin makamashi na ƙasa daban-daban da kuma doka.

Daga cikin mitoci kubik biliyan 167.7 na iskar gas da Turai ta shigo da su daga Rasha a shekarar 2020, Jamus ta sayi mafi yawan mita cubic biliyan 56.3 ,  sai Italiya da biliyan 19.7 sai Netherlands mai biliyan 11.2.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending