Connect with us

Wasanni

Premier League: An yi watsi da bukatar Everton a kan jan katin dan wasan ta

Published

on

Hukumar gasar Premier ta kasar Ingila ta yi watsi  da daukaka karar da Everton ta yi har sau biyu a kan jan katin da aka baiwa dan wasan tsakiyar ta Allan a wasan da Newcastle ta doke ta da ci 1-0.

Alkalin wasan Craig Pawson ne ya bai wa dan wasan na Brazil jan kati, bayan ya kayar da Allan Saint-Maximin na Newcastle.

Amma, bayan mataimakin alkalin wasa na bidiyo (VAR) ya gaya masa cewa, ya sake duba laifin da aka yi a kan na’urar dubawa, a Pawson ya inganta shi zuwa ja.

Everton ta ce, “An yi watsi da bukatarsu ta soke wannan shawarar tare da kara na biyu na rage hukuncin haramtawa fiye da kima”.

Yanzu Allan ba zai buga wasan kusa da na karshe na cin kofin FA da za a yi a Goodison Park da Crystal Palace ranar Lahadi, da kuma wasannin Premier da za a yi a West Ham da Burnley.

Everton ta samu uzuri daga shugaban alkalan wasa Mike Riley a kakar wasa ta bana bayan da aka hana ta bugun fanareti a wasan da Manchester City ta doke su da ci 1-0 a watan jiya.

A wancan lokacin VAR ba ta gaya wa alkalin wasa Paul Tierney ya sake duba hukuncin da ya yanke ba.

Kafin a yi watsi da karar da wata hukumar mai zaman kanta ta yi watsi da karar, kocin Toffees, Frank Lampard ya ce: “Ba mu bukatar uzuri, amma kawai mu dubi hukuncin a can baya kuma ya isa a ba da izinin jan kati, ko shakka babu”.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending