Manyan Labarai
Labarai a Takaice na yau 16-04-2019
Wani Malami a tsangayar sashen tarihi da hulda da kasashen waje a jami’ar Yusuf Maitama Sule dake Kano, Malam Murtala Mustapha, ya yi kira ga matasa cewa da su tashi tsaye wajen rungumar al’adun Hausa maimakon aron na Bature ko wani Yare.
Malam Murtala Mustapha, ya bayyana hakan ne yayin wani taro na musamman da Jami’ar ta shirya a kan abubuwan da suka shafi Kano tin daga zamanin Bagauda har zuwa yanzu.
Ya ce “cigaban da jihar Kano ta bayar a nahiyar Afrika ya ta’allaka ne ta hanyar bunkasa al’adun Hausa”, sannan kuma ya bukaci matasa dasu tashi tsaye wurin neman illimi don tsiratar da rayuwar su.
Kungiyar bunkasa illimi da cigaban demokradiyya da samar da daidaito a zamantakewa SEDSAC, tarayya bisa matakin da ta dauka na tura jami’an soji a jihohin Zamfara da Katsina da kuma Kaduna bisa rikicin da yankunan ke fama da su musamman ma masu garkuwa da mutane.
A wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai kunshe da sa hannun babban Daraktan kungiyar, Kwamrade Hamisu Kofar Na’isa ya sanyawa hannu, ya ce “rashin samar da tsaro babban kalubale ne a fadin kasar nan bisa yadda masu garkuwa ke amfani da mugan makamai a hannun su”.
Kakakin hukumar dake kula da gidajen yari na jihar Kano, DSP Musbahu Lawan Kofar Nasarawa, ya ce “Kofar hukumar a bude ta ke wurin tallafawa daurarru musamman a watan Azumin Ramadan mai karatowa”.
yayin zantawarsa jim kadan bayan kammala shirin Shari’a a aikace na gidan Rediyon Dala, DSP Musbahu Lawan Kofar Nasarawa, ya ce “gidan yari kaddara ce ke kai mutum a don haka mutane su guji kyamatar daurarru wanda kowa zai iya tsintar kansa a wannan wuri.
Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi gwamnatin jiha da ta fara amfani da wurin sauke kaya da gwamnatin tarayya ta tanada a yankin Zawachiki dake karamar hukumar Kumbotso.
Kiran ya biyo bayan amince da rahoton hadin gwiwa da shugaban kwamatin ayyuka da sufuri na majalisar, Abubakar Zakari Muhammad, ya gabatar a kan dalilan dake kawo cinkoson manyan motocin dakon kaya a cikin kwaryar birnin Kano insa yace masu kayan ba sa kiyayewa da dokokin daukar kayan da hukumar Kwastan ta gindaya masu.
Majalisar dokokin jihar Kano, ta amince da rahoton da kwamatin kula da harkoki addini ya ganatar mata a kan kudirin dokar gyara sashi na 27 na kundin dokar da ta kafa hukumar Shari’a ta jiha ta shekarar 2002.
Shugaban majalisa, Kabiru Alhassan Rurum ne, ya bayyana hakan a yin zaman majalisar da ta yi.
Dan majalisar tarayya ai wakiltar Kunci da Tsanyawa, Injiniya Sani Bala Tsanyawa, ya bayyana cewa karanci wutar lantarki da ake fuskanta a jihar , ya na da nasabane da matsalar saka babban injin Taransifoma a daya daga cikin manyan tashoshin raba wuta dake karamar hukumar Kumbotso Wanda har yanzu ba’a kammala aikin.
Da yake zantawa da gidan Rediyon Dala, injiya Sani Bala ya ce a ziyarar da suka kai tashoshin raba wuta dake Jaba da Sharoro da Kayanji su na da karfin bada wuta sama da abinfa ake bukata, wanda hukumar rarraba wutar lantarki ta kasa itace har yanzu ba ta samar da wutar ga KEDCO ba.
Za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a cikin labaran da muke kawo muku a cikin wannn shafi.

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Manyan Labarai
An ga watan ƙaramar Sallah a Najeriya – Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya, inda za a yi karamar Sallah gobe Lahadi.
Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yayin jawabin da ya gabatar a cikin daren Asabar ɗin nan, ya ce sun samu rahotannin ganin watan ne daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce daga cikin guraren da aiko musu da ganin jinjirin watan na Shawwal akwai Zazzau, da kuma daga Sarkin Dutse, da Arugungu, da kuma Shehun Borno, da dai sauran gurare daban-daban na Najeriya.
Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su gabatar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali, tare da taimaka wa mabuƙata.
Tashar Dala FM Kano ta ruwaito cewa, biyo bayan sanarwar fadar mai alfarma Sarkin Musulmi, ya kasance ranar Lahadi take 1 ga watan Shawwal na shekarar 1446, wato ranar ƙaramar Sallah.

Manyan Labarai
Shugaba Tinubu da Sifeton Ƴan Sanda ku bi wa mutanen mu da aka yi wa kisan gilla hakƙin su – Rt. Hon. Rurum

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Rabo, Kibiya da Bunkure, Kabiru Alhassan Rurum, ya bayyana kaɗuwar sa bisa kisan gillan da aka yi wa wasu Mafarauta su kusan 16, a garin Uromi da ke jihar Edo, a lokacin da suke hanyar su ta komawa Kano daga jihar Rivers.
Honarable Kabiru Rurum, ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da aka aikowa Dala FM Kano a ranar Asabar, ya ce daga cikin mutanen da aka ƙona akwai mutum 11 da suka fito daga mazaɓun yankin sa na Kibiya da Bunkure, inda wasu 6 suka samu muggan raunuka suna karɓar Magani yanzu haka a jihar Edo.
A cewar Ɗan Majalisar, “Wannan abu da matasan garin Uromi a jihar Edo, suka yi ya saɓa da dokar kasa, kuma mummunan laifi ne, a don haka za mu bi kadin hakƙin mutanen mu da aka kashe a kuma waɗanda aka jikkata, “in ji shi“.
Kabiru Rurum, ya ce a matsayinsa na wakilin mutanen da aka kashe a majalisar Wakilai ta ƙasa, yana kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da babban Sifeton ƴan sanda, da su yi duk mai yiyuwa wajen ganin an kamo waɗanda suka yi wannan aika-aikar tare da hukunta su, da kuma biyan diyya ga iyalan waɗanda suka rasu da kula da waɗanda suka jikkata.
“Kasancewar wannan bashi ne na farko da ake samun wasu ɓata gari na tare matafiya akan hanya da basu ji ba basu gani ba su kashe su, a don haka muna fatan wannan karon gwamnati da sauran hukumomin tsaro za su ƙaddamar da ƙwaƙƙwaran bincike don ɗaukae mataki kamar yadda dokar kasa ta tanada, “in ji Rurum”.
Ɗan majalisar ya kuma jajantawa dukkanin al’ummar jihar Kano musamman Iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar Allah ya gafarta musu yasa Jannatul Firdausi makomar su, su kuma waɗanda suka jikkata Allah ya basu lafiya.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su