Connect with us

Manyan Labarai

Labarai a takaice na yau Laraba 17-04-2019

Published

on

4:14pm Hukumar kula da harkokin shari’a da ladaftarwa NJC ta tabbatar da Justice Nura Sagir Umar a matsayin sabon babban jojin jihar Kano.

Kakakin kotunan Kano, Baba Jibo Ibrahim ne ya bayyana hakan cikin zantawarsa da wakilin mu Yusuf Nadabo Isma’il.

Rundunar ‘yansandan jihar Kano, ta fara gudanar da bincike kan wata mata mai suna Hassana Lawan mai shekaru 15 wacce ake zargin ta da zubawa mijinta mai suna Sale Abubakar mai shekara 33 shinkafar bera a cikin abinci a unguwar Bechi dake karamar hukumar Kumbotso.

A cikin wata sanarwa mai kunshe da sa hannun Kakakin rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta ce yanzu haka mai gidan ta Sale Abubakar, ya na asibitin Murtala ana duba lafiyar sa ita kuma matar ta sa an tsare ta ana cigaba da tuhumar ta dazarar sun kammala za a gurfanar da ita a gaban kuliya.

Limamin masallacin Juma’a na Triumph Malam Lawan Abubakar, ya yi Kira ga al’umma da su rungumi turbar addu’a da ayyuka na gari, domin ta hakane za’a sami saukin yawan satar mutane da sunan kudin fansa da ake samu a wasu sassan kasar nan.

Da yake zantawa da wakilin mu Ahmad Rabi’u Ja’en, Malam Lawan ya kuma ce “matukar hukuma za ta rinka zartas da hukunci ga irin wannan mutane to babu shakka sai an samu raguwar yin garkuwa da mutane a matsayin a matsayin kudin fansa.

Hukumar Hisba a jihar Kano, ta kau want simame wata mashayar barasa dake ‘yan Katako a unguwa Uku a wani yunkuri na dakile aikata miyagun ayukan badala a sassan jihar Kano.

Yayin simamen dai jami’an hukumar Hisba sun sami nasarar kama mai siyar da barasa tare da masu shanta Wanda hukumar ta ce za ta kai su kotu domin girbar abun da suka shuka.

11:00am Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta ce ta fara gudanar da bincike a kan rasuwar wasu matasa biyu da jirgin kasa ya bi takan su a daren Litinin din da ta gabata sakamakon barci da su ka yi a kan titin jirgin bisa shaye-shaye da ake zargin sun yi a lokacin.

Kakin rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ya na mai cewa ”jami’an ‘yan sanda ne su ka dauke gawar matasan biyu zuwa Asibiti wanda likita ya tabbatar da mutuwar su”, a hannun guda kuma mun tuntubi hukumar kula da sifirin jirgin kasa dake Kano sai dai ta ce babu abin da za ta ce a kan lamarin.

Kotun Majistret mai lamba 35 karkashin mai shari’a, Sunusi Usman Atana, ta fara sauraron wata Kara da ‘yansanda su ka gurfanar da wani mutum mai suna Sulaiman Aliyu wanda ake zargin sa da laifin zamba cikin aminci da cuta wanda laifukan sun saba da sashi na 312 da na 322 kundin penal code.

Tun da fari dai wani mai suna Alh Sabi’u Muhammad ne ya shigar da Kara cewa ya baiwa Sulaiman naira miliyan daya da dubu 200 da 26 don ya yi masa safarar shinkafa buhu dari da hamsin da uku Amma Sulaiman tasarrafi da kudin sai dai kuma ya musanta zargin Wanda tini kotun ta sanya ranar 15 ga watan gobe don kawo shaidu.

Shugaban kungiyar masu sana’ar siyar da Nono a kasuwar Kofar Wambai a jihar Kano, Malam Muhammad Lawan Alaramma, ya ce “kungiyar su ta dauki gabarar tsaftace harkokin sana’ar siyar da Nono a wani mataki na zamanantar da sana’ar siyar su.

Yayin zanatawarsa ga manema labarai da ya yi, Malam Muhammad Alaramma, ya ce”tuni kungiyar ta dauki matakin yin rijista ga masu gudanar da sana’ar nono don magance bata gari a harkar.

Manyan Labarai

Uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a Kano sun rasu

Published

on

Rahotanni da dumi-ɗumin sa na bayyana cewar yanzu haka uku daga cikin mutane sama da 20 da wani matashi ya cinnawa Wuta cikin wani masallaci a unguwar Larabar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a Kano sun rasu.

Wani mazaunin garin ya shaidawa Dala FM Kano, da tsakar ranar Larabar nan cewar, daga cikin mutane ukun da suka rasu har da limamin da ya jagorancin sallar asubar wannan rana, wanda a lokacin ne matashin ya cinna musu wutar lamarin da jikin su mutanen sama da 20 ya sassaɓule.

Idan dai ba’a manta ba matashin ya cinnawa mutanen wuta ne bayan da ya watsa Fetur cikin masallacin yayin da suke tsaka da sallar Asubah, ta wannan rana, wanda tuni jami’an tsaron ƴan sanda suka cika hannun su da shi.

Matashin dai ya ce ya cinnawa mutanen wutar ne biyo bayan wata magana da suke faɗa masa wanda ransa baya daɗi, ina ya sayo Fetur a cikin wani Galan lamarin da yaje ya kunna musu wutar, duk da shima hannayen sa biyu sun ƙone.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun kama matashin da ya kunnawa mutane sama da 20 Wuta a cikin wani masallaci – Ƴan Sandan Kano

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta tabbatar da kama wani matashi da ake zargi da cinnawa wasu mutane Wuta, a lokacin da suke tsaka da Sallar Asubar yau Laraba, a cikin wani Masallaci a garin Larabawar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a Kano.

Kakakin rundunar ƴan sandan SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya aikowa Dala FM Kano, a yau Laraba, ya ce bayan samun rahoton faruwar al’amarin ne Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Muhammad Usaini Gumel, ya tura tawagar jami’an su inda suka kai ɗaukin gaggawa.

Matashin da ake zargin mai suna Shari’u Abubakar ɗan shekaru shekaru 38, ya ce shine ya siyo Fetur ya kunna wutar inda ya wurgata a cikin masallacin, lamarin da ya sa mutane da dama suka ƙone a sassan jikin su.

“Aƙalla mutane 24 ne suka ƙone bayan da matashin ya kunna musu wutar a cikin masallacin, wanda tuni jami’an mu suka kai su asibitin Murtala Muhammad da ke Kano, inda suke ci gaba da samun kulawar likitoci, “in ji SP Kiyawa”.

Koyawa, ya kuma ce daga binciken farko da suka fara matashin ya tabbatar da cewa shine ya sayo Mai a gidan Mai a cikin wata roba, yazo ya kunna wutar, biyo bayan wani rikicin gado da a tsakanin sa da wasu daga cikin mutanen yankin su, inda shima hannayen sa biyu suka ƙone.

Continue Reading

Manyan Labarai

Sama da mutane 20 ne suka ƙone a sassan jikin su bayan da ake zargin wani abu ya fashe a cikin wani masallaci da ke Kano

Published

on

Rahotanni na nuni da cewa an yi zargin fashewar wani abu da asubahin wannan rana ta Laraba, a garin larabar Abasawa da ke ƙaramar hukumar Gezawa a jihar kano, wanda kuma ya jikkata sama da mutane 20, sakamakon ƙonuwa a sassan jikinsu.

Yanzyu haka dai da yawa daga cikinsu sun fara karɓar agajin
gaggwa a babban asibitin ƙwararru na Murtala Muhammad, da ke Kano, kamar yadda wani ganau ya shaidawa
gidan rediyon Dala FM, lokacin da ya ziyarci asibitin a safiyar wannan
rana.

Sai dai wani da ya tsallake rijiya da baya mai suna Yusuf Abdullahi, ya ce yana cikin masallacin lokacin da lamarin ya faru suna tsaka da Sallah Asuba aka kunna wutar daga waje inda aka cillota cikin masallacin, saɓanin abin fashewar da wasu suke faɗa.

Ya kuma ce, “Allah ne kawai ya bani ikon fita Amma mutane da yawa ciki har da yan uwana guda biyu lamarin ya rutsa da su, kuma wutar ta yi musu illa babba saboda ko kasan mutum wallahi idan ka gan shi wallahi ba za ka iya gane shi ba”. Inji Yusuf Abdullahi”.

Wakilin Dala FM, Ibrahim Abdullahi Soron Ɗinki, ya tuntuɓi mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta wayar tarho, sai dai ya ce yanzu haka
yana kan aikin tattara bayanai akan al’amarin, wanda rundunar
za ta fitar nan gaba kaɗan.

Continue Reading

Trending