Ilimi
Rahoto: Ƙorafi da nacin ƴan jarida ya sa an gina makarantar Tudun Kaba

Al’ummar garin Tudun Kaba, sun bayyana farin cikin su sakamakon gina musu ajujuwa guda biyu a makarantar Firamare da ke yankin, bayan wani rahoto da gidan rediyon Dala ya yi dangane da matsalar rashin ajujuwa da ke suke fuskanta.
Shugaban kungiyar iyaye da malamai yara na makaranatar, malam Yakubu Muhammad, a zantawarsa da wakilin mu na ‘yan Zazu, Abba Isah Muhammad, ya bayyana cewar, a baya dariya ake yi musu dangane da yadda makarantar take, amma yanzu mahukunta sun ji kokensu har aka aka gina musu ajujuwa.
Domin jin cikakken rahoton saurari wannan.

Addini
Abubuwan da ya kamata mu yi a lokacin da muke cikin fushi.

- Fushi daga shaidan yake
- Mu yawaita zama da Alwala da kuma ambaton Allah
- Mu guji daukar hukunci lokacin da muke cikin fushi .
A shafin sa na facebook, Falalu Dorayi yayi tsokaci kan abubuwan dake jawo fushi, da kuma hanyoyi kauce musu kamar haka
Tasirin fushi a zucivar Dan Adam na iva haifar da masifu da abubuwa marasa dadi iri iri, ciki harda kisan kai.
Duk Lokacin da Dan Adam yake cikin fushi ko wani vanayi na bacin rai,Tabbas wannan mutumin na samun bakuncin Shaidan kusa da zuciyarsa, kuma duk hukuncin da zai yi a wannan lokacin ba zai zamo mai inganci ba,ma’ana zai dauki hukunci mara dadi.
Idan muka samu kanmu a irin wannan yanayin Ma’aiki Rasulullah (SAW) Ya bamu mafita:
- Mu daura Alwala
- Mu yawaita fadin “A’udhu billahi minashaytaan-ir-rajeem”
- Idan a tsaye muke mu zauna, idan bamu daina fushin ba kuma mu kwanta.
Kada mu biyewa zuciya, mu kasance masu hakuri.
Rahoto: Koyi da halayen Annabi ne nuna tsantsar kaunar sa – Limamin Tukuntawa
Ubangiji Yana son masu hadiye fushi da yafiya lokacin da aka fusata su.
Mu duba; (Ali Imran 3:134)
Allah Yasa mu dace

Ilimi
Ba Aiki Ba Biya: Mu na nan a kan bakar mu – Gwamnati

Yayin da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU ke gudanar da zanga-zangar lumana a faɗin jami’o’in ƙasar nan, domin nuna rashin jin daɗinsu game da rashin biyansu albashin watannin da suka kwashe suna yajin aiki, gwamnatin ta ce, ba za ta biya malaman albashin aikin da ba su yi ba.
Ministan ilimin ƙasar Malam Adamu Adamu ne ya bayyana haka ranar Laraba, bayan taron majalisar zartarwa da shugaban ƙasar ya jagoranta a fadar gwamnatin da ke Abuja.
Yayin da yake martani game da iƙirarin da shugaban ASUU ya yi na cewa gwamnati na son mayar da malaman jami’ar ma’aikatan wucin-gadi, ministan ya ce gwamnatin ba ta da wannan niyyar.
“An janye yajin aiki, kuma gwamnati ta biyasu haƙƙin iya aikin da suka yi. Ina tunani wannan shi ne matsayin gwamnati, cewa ba wanda za a biya albashin aikin da bai yi ba, sun yi aiki na kwanaki, kuma gwamnati ta biya su haƙƙinsu kwanakin da suka yi”, in ji Adamu Adamu.

Ilimi
Daliban jami’ar ABU za su koma makaranta ranar 24 ga watan Oktoba

Biyo bayan dakatar da yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU ta yi na tsawon watanni takwas, jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), ta sanar da ranar 24 ga Oktoba, 2022 a matsayin ranar da za ta ci gaba da gudanar da ayyukan ilimi.
Majalisar Dattawa ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ce ta cimma matsayar.
Daraktan hulda da jama’a na Jami’ar, Auwalu Umar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, inda ya ce, an cimma matsayar ne a taron gaggawar da ta gudanar 516 biyo bayan dakatar da yajin aikin da ASUU ta yi.
Sanarwar ta ce, a zamanta na farko a ranar 25 ga watan Nuwamba, 2021, a zamanta 513, majalisar ta amince da ranar, inda ta kara da cewa, saboda yajin aikin ASUU da aka tsawaita, a yanzu majalisar ta sauya ranar zuwa 24 ga watan Oktoba 2022.
Ya ce, jami’ar za ta koma ranar Litinin, 24 ga watan Oktoba, 2022, inda ta kara da cewa an shawarci dalibai da su lura da sabuwar ranar, saboda za a fara gudanar da harkokin karatu na yau da kullun.
Haka kuma ta yi kira ga daliban da su rike sabuwar kalandar jami’a ta yadda za ta yi musu jagora domin ba za a samu uzuri ga duk dalibin da ya yi biris da ranar da za a ci gaba da karatu ba.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai3 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai3 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai3 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano