Connect with us

Labarai

Shiyyar Arewa maso Yamma sun fi kowa yin katin zaɓen 2023 – INEC

Published

on

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana cewa, shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu-maso-Yamma ne ke kan gaba wajen yin rajistar masu kada kuri’a da 22,672,373 da 18,332,191.

Wani sabon rahoto da aka wallafa a shafin internet na INEC ya nuna cewa, mutane 96,303,016 ne suka yi rajista kafin a dakatar da rajistar masu zabe a ranar 31 ga watan Yuli.

A shekarar 2019, hukumar ta yi wa masu jefa kuri’a 84,004,084 rajista. Alkaluman da hukumar zabe ta INEC ta fitar a shekarar 2022 sun nuna an samu karuwar masu rajista da yawansu ya kai miliyan 12,298,932 gabanin babban zaben shekarar 2023.

Arewa-maso-Yamma, wadda ta kunshi jihohi bakwai (Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sokoto da Zamfara), nada masu zabe miliyan 22,672,373. Yankin Kudu-maso-Yamma da ya kunshi Legas, Oyo, Ondo, Osun da Ekiti sun bi sahun masu kada kuri’a miliyan 18,332,191.

Arewa ta tsakiya ta zo na uku da 15,680,438 da suka yi rajista, dan sama da Kudu maso Kudu da 15,299,374. Yankin Arewa-maso-Gabas na da masu jefa kuri’a 12,820,363 ya zuwa yanzu. Kudu-maso-Gabas na da mutane 11,498,277 da suka cancanci kada kuri’a.

Bayanai na INEC sun kara nuna cewa, sama da kashi 50 cikin 100 (8,854,566) na sabbin masu kada kuri’a 12,013,068 ne suka yi rajista da kansu, wasu kuma (3,444,378) sun yi rajista ta shafin hukumar.

Hakanan, sama da sabbin masu jefa ƙuri’a miliyan 12 sun ƙunshi maza 6,074,078 da mata 6,224,866.

Duk da cewa, kungiyoyin kare hakkin jama’a da jam’iyyar APC mai mulki, sun yi yunkurin tsawaita rajistar masu kada kuri’a (CVR), INEC ta ƙara wa’adin yin rajistar wanda ya ƙare a ranar 31 ga watan Yuli.

Tun da farko dai INEC ta kara tsawaita rajistar CVR daga ranar 30 ga watan Yuni zuwa 31 ga watan Yuli.

Labarai

Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.

Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.

“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi

Published

on

Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.

Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.

Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.

Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.

Continue Reading

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Trending