Labarai
Shiyyar Arewa maso Yamma sun fi kowa yin katin zaɓen 2023 – INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana cewa, shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu-maso-Yamma ne ke kan gaba wajen yin rajistar masu kada kuri’a da 22,672,373 da 18,332,191.
Wani sabon rahoto da aka wallafa a shafin internet na INEC ya nuna cewa, mutane 96,303,016 ne suka yi rajista kafin a dakatar da rajistar masu zabe a ranar 31 ga watan Yuli.
A shekarar 2019, hukumar ta yi wa masu jefa kuri’a 84,004,084 rajista. Alkaluman da hukumar zabe ta INEC ta fitar a shekarar 2022 sun nuna an samu karuwar masu rajista da yawansu ya kai miliyan 12,298,932 gabanin babban zaben shekarar 2023.
Arewa-maso-Yamma, wadda ta kunshi jihohi bakwai (Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sokoto da Zamfara), nada masu zabe miliyan 22,672,373. Yankin Kudu-maso-Yamma da ya kunshi Legas, Oyo, Ondo, Osun da Ekiti sun bi sahun masu kada kuri’a miliyan 18,332,191.
Arewa ta tsakiya ta zo na uku da 15,680,438 da suka yi rajista, dan sama da Kudu maso Kudu da 15,299,374. Yankin Arewa-maso-Gabas na da masu jefa kuri’a 12,820,363 ya zuwa yanzu. Kudu-maso-Gabas na da mutane 11,498,277 da suka cancanci kada kuri’a.
Bayanai na INEC sun kara nuna cewa, sama da kashi 50 cikin 100 (8,854,566) na sabbin masu kada kuri’a 12,013,068 ne suka yi rajista da kansu, wasu kuma (3,444,378) sun yi rajista ta shafin hukumar.
Hakanan, sama da sabbin masu jefa ƙuri’a miliyan 12 sun ƙunshi maza 6,074,078 da mata 6,224,866.
Duk da cewa, kungiyoyin kare hakkin jama’a da jam’iyyar APC mai mulki, sun yi yunkurin tsawaita rajistar masu kada kuri’a (CVR), INEC ta ƙara wa’adin yin rajistar wanda ya ƙare a ranar 31 ga watan Yuli.
Tun da farko dai INEC ta kara tsawaita rajistar CVR daga ranar 30 ga watan Yuni zuwa 31 ga watan Yuli.

Hangen Dala
Rashin wuta: Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.
Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.
Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.
Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.
Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.
Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.
Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.
Hangen Dala
Rashin wuta:- Muna cikin mawuyacin hali – al’ummar Kano, Katsina da Jigawa

Al’ummar jihohin Kano, katsina da Jigawa na fuskantar yanayi mara dadi, Sakamakon karancin samun wutar lantarki daga hukumar KEDCO.
Al’ummar jihohin sun ce iya sa’o’i uku kacal suke samun wutar, wanda hakan ke haifar musu da nakasu a harkokin kasuwancin su.
Wani bincike da jaridar Daily Trust tayi ta ambato yadda masu kananan masana’antu irin su Walda, Cajin Waya, Kankara da masu sana’ar dinki da dai sauran kananan sana’o’i dake amfani da wutar lantarki sun shiga mawuyacin hali.
Kazalika rashin wutar ya shafi hatta bangaren ruwan sha, dama masu sana’ar sayar da Ruwa a irin yankunan Hotoro da sauran irin wuraren dake sayen ruwa, Inda yanzu haka ruwan yayi tashin gwauron zabi a kowace jarka.
Koda dai ana ta bangaren hukumar rarraba hasken wutar lantarkin me kula da shiyyar Kano, Katsina da Jigawa KEDCO sun nemi afuwar al’umma.
Idan za’a tuna dai a makon jiya ne Ministan Wutar lantarki yace ‘yan Nigeria Miliyan 150 na samun wadatacciyar wutar lantarki.
Sai dai kuma a jihohi irin su Kano, Katsina da Jigawa na bayyana damuwa kan karancin Wutar, Inda suka ce bata wuce ta sa’o’i uku suke samu a kowa ce rana.
Labarai
Ci gaba ba ya zuwa sai an samu haɗin kan al’umma – Dagacin Ja’en

Dagacin garin Ja’en da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, Alhaji Isma’il Sa’ad Usman, ya ce hadin kai ne kaɗai zai kawo ci gaba ga kowa ce irin al’umma.
Dagacin ya bayyana hakan ne Jim kaɗan bayan wani taron masu Ruwa da tsaki na Garin Ja’en, wanda Hakimin Gundumar Ɗorayi Barde Kerarriya Alhaji Shehu Kabir Bayero ya shirya, aka gudanar a yankin Ja’en a ƙarshen makon da ya gabata.
“Dukkanin wani ci gaba ba ya zuwa har sai an samu haɗin kan kowa ne bangare na al’umma, “in ji Dagacin”.
Wakilin Dala FM Kano, Ahmad Rabi’u Ja’en ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar dukkanin bangarori, na unguwannin Ja’en, da suka haɗar da kungiyar mafarauta da maharba dabma kungiyar malaman makaranta.
-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su