Connect with us

Ilimi

Ba mu da kudin motar komawa Jami’a – ASUU

Published

on

Shugaban kungiyar malaman Jami’o’i ta kasa, Farfesa Emmanuel Osodoke, ya ce, mambobin kungiyar za su fuskanci wahala wajen komawa jami’o’insu a ranar Litinin saboda ba su da kudin motar komawa.

Shugaban na ASUU ya bayyana haka ne a jiya Lahadi, yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels dangane da janye yajin aikin na ASUU.

Farfesa Osodoke, ya ce, a baya malaman Jami’a na zama a gidajen da aka tanada musu kusa da makaranta, amma a yanzu ba haka lamarin yake ba domin suna zaune ne nesa da Jami’oin da suke koyarwa saboda yawancinsu basa samar musu wuraren zama.

“A can baya, malami zai iya taka wa da kafa yaje makaranta saboda suna zaune a cikin gidaje da aka tanada musu, amma a yanzu lamarin ya sauya, inda suke tafiyan kilomitoci 20 zuwa 30 kafin isa makaranta. Ta ya ya za su iya biyan kudin mota zuwa aiki,’‘ in ji Osodoke.

Ya kuma ce, za su fuskanci wahalhalu wajen biyan kudin motar komawa aiki domin koyar da dalibai sbaoda ba a biya su ba har na tsawon wata takwas.

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Ilimi

Za’a daga likafar BMC zuwa Diploma – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tace nan bada jimawa ba za’a daga likafar makarantar koyon aikin jarida a matakin farko wato BMC ta Goron Dutse zuwa tsarin Diploma.

Mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam ne ya tabbatar da hakan lokacin da yake jawabi a wurin taron da kungiyar tsaffin daliban makarantar suka shirya.

Kwamred Aminu Abdussalam ya kuma ce nan bada jimawa ba makarantar za’a daga matsayin karatun daga Certificate zuwa Diploma, kamar yadda makarantar ta bukata.

Kazalika yace gwamnatin Kano za ta cigaba da lura da dukkanin kayan koyo da koyarwa har ma da ababen hawa na hukumar ilimin manya ta Kano, wato Agency for mass Education wadda a cikin ta ake karatun na jarida.

Taron dai wanda shi ne karo na farko da gamayyar kungiyar daliban ta shirya tun bayan kafuwar makarantar shekaru 38 da ta gabata, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗar da Kwamishinan ilimi na Kano da Kwamishinan yada labarai da kwamishiniyar mata da mai baiwa gqamna shawara kan harkokin yada labarai.

Kazalika taron ya samu halartar Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da tsaffin malaman makarantar da kuma shugabannin kafafen yada labarai na Kano.

A yayin taron dai shugaban kungiyar taaffin daliban Ismaila Ammai me Zare ya kaddamar da wani tsari na tallafawa makarantar da abin zama mai taken ( ka dawo da kujerar ka ).

Continue Reading

Trending