Connect with us

Ƙasashen Ƙetare

Da Duminsa: Firaministar Birtaniya ta yi murabus

Published

on

Liz Truss ta sanar da yin murabus daga mukaminta na Firaminista.

Da take magana a wajen titin Downing, ta ce, ta shaida wa Sarki Charles cewa ta yi murabus a matsayin shugabar jam’iyyar Conservative Party.

Liz Truss ta ci gaba da cewa ta gana da shugaban kwamitin 1922 Sir Graham Brady a yau.

Sun amince za a gudanar da zaben shugaban Firaminista a cikin mako mai zuwa, inda suka kara da cewa za ta ci gaba da kasancewa a matsayin firaminista har sai an zabi wanda zai gaje ta.

“Ban taba ganin wani abu makamancin haka ba. Bari mu fayyace abin da ya faru jiya Truss ta gaya mana cewa ta kasance mayaka”.

Sai dai matakin rudanin gwamnati da majalisar dokoki da jam’iyyar Conservative ya sa Truss ta kai matsayin da ta san ba za ta iya ci gaba ba.

Abin da ke faruwa a yanzu shi ne saurin juyawar mulki da muka gani a wannan zamani.

Wannan canjin saurin walƙiya ne. Tambayar ita ce ko jam’iyyar Conservative za ta iya hada kai da wani sabon shugaba da kuma ko jam’iyyar za ta iya kaucewa babban zabe.

A watan Oktoba za mu sami Firaminista ta uku a shekara.

Wannan lamari ne da ba a taba ganin irinsa ba, kuma gajeriyar wa’adi ne na Firayim Minista da kuma rikicin da ba a taba ganin irinsa ba a siyasar Burtaniya.

Shugabar jam’iyyar Labour Keir Starmer ,ta bukaci a gudanar da babban zabe “yanzu” bayan Liz Truss ta sanar da murabus din ta a matsayin firaminista.

Truss ta daɗe tsawon watanni biyu a kan kujerar ta. Ta doke Rishi Sunak da kuri’u 81,326 zuwa 60,399 a zaben cikin gida bayan Boris Johnson ya yi murabus a watan Yuli.

Ta kasance shugaba na hudu na jam’iyyar Conservative a gwamnatin Birtaniyya tun daga shekarar 2015, inda ya yi alkawarin fitar da damar Birtaniyya ta hanyar samun ci gaba da kuma kawar da cikas da ke kawo wa kasar baya.

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji Sun yi juyin Mulki a Gabon

Published

on

Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na kasar Gabon tare da sanar da karbi mulki.

Sun ce sun soke sakamakon zaben da ka gudanar ranar Asabar, inda aka ayyana shugaba Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukumar zaben ta ce Mr Bongo ya samu nasara ne da kasa da kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kada a zaben da ‘yan adawa suka ce an tafka magudi.

Sun Kuma ce Hambarar da shi zai kawo karshen mulkin shekaru 53 da iyalan gidansu ke yi a Gabon.

Sojoji 12 ne suka bayyana a gidan talabijin dake sanar da soke sakamakon zaben tare da rusa dukkan hukumomin kasar.

Daya daga cikin sojojin ya fada a tashar talabijin ta Gabon 24 cewa, “Mun yanke shawarar kare zaman lafiya ta hanyar kawo karshen mulkin da ake yi a yanzu.”

Mr Bongo ya hau karagar mulki lokacin da mahaifinsa Omar ya rasu a shekara ta 2009.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

Sojoji sunyi juyin Mulki a jamhuriyar Nijar

Published

on

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar na cewa Sojojin Kasar sun yi juyin Mulki, tare da sanar da kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum.

Cikin sanarwar da suka bayar a gidan telebijin din Kasar, jagoran tawagar sojojin Kanal Amadu Abdramane yace “mun kawo karshen mulkin shugaba Muhammad Bazum tare da karbe dukkanin Wani Iko”.

Sojojin dai sun bayar da dalilin halin rashin tabbas da Kuma Matsin tattalin arziki a kasar.

Tuni dai sojojin suka garkame dukkanin iyakokin Kasar tare da Sanya dokar takaita zirga zirga daga karfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Tun a safiyar laraba ne dai aka wayi gari da fara wancan yunkuri, Wanda yanzu haka ta tabbata, Kasar Nijar na hannun sojoji, Wanda shi ne Karo na hudu ana gudanar da juyin mulkin a jamhuriyar Nijar.

Continue Reading

Ƙasashen Ƙetare

An tsaurara tsaro a fadar shugaban Kasar Nijar

Published

on

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar, na nuni da cewa dakarun da ke gadin fadar shugaban ƙasa sun rufe duk wata hanyar shiga fadar a wani lamari da ba a kai ga ganowa ba.

Sai dai rahotanni na cewa yanzu haka wasu daga cikin tsofaffin shugabannin ƙasar ta Nijar na tattaunawa da sojojin domin sasanta lamarin.

Karin bayani nan tafe….

Continue Reading

Trending