Connect with us

Wasanni

Modric zai buga gasar cin kofin duniya na hudu da Croatia

Published

on

An saka dan wasan Real Madrid Luka Modric a cikin ‘yan wasan kasar Croatia a wasan da zai kasance karo na hudu a gasar cin kofin duniya.

Dan wasan tsakiyar mai shekaru 37, wanda aka zaba a matsayin gwarzon dan wasan da ya lashe gasar a Rasha 2018, ya kuma wakilci Croatia a Jamus 2006 da Brazil 2014.

Dan wasan Tottenham Ivan Perisic da dan wasan tsakiya na Chelsea Mateo Kovacic suma suna cikin ‘yan wasa 26.

Croatia wadda ta zo ta biyu a Rasha tana rukuni na uku a Qatar, tare da Belgium da Canada da kuma Morocco.

Nikola Vlasic na West Ham, wanda a halin yanzu yake zaman aro a Torino, yana cikin tawagar, tare da masu tsaron baya na gasar Premier ta Scotland Borna Barisic, na Rangers, da Josip Juranovic na Celtic.

Dejan Lovren, mai shekara 33, tsohon mai tsaron baya na Liverpool da Southampton, wanda yanzu ke taka leda a Zenit St Petersburg, ya dawo bayan buga wasan karshe na gasar cin kofin duniya na 2014 da 2018.

Croatia ta doke takwararta Gareth Southgate ta Ingila a wasan kusa da na karshe a Rasha kafin ta sha kashi a hannun Faransa da ci 4-2 a wasan karshe.

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending