Labarai
An nemi mu bayar da Naira miliyan 10 kafin a saki gawar dan uwan mu – Dan Uwa
‘Yan bindiga sun bukaci a biya su Naira miliyan 10, kafin su sako gawar wani Obadiah Ibrahim da a ka yi garkuwa da su a Sabon Gaya a farkon watan Oktoba.
A cewar Kefas Obadiah, dan uwa ga mamacin, tuni aka baiwa ‘yan fashin Naira miliyan uku a matsayin kudin fansa.
Ya koka da yadda aka yi garkuwa da dan’uwansa a hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Abuja a wani kauye, Sabon Gaya a farkon watan Oktoba, inda ya ce bayan sun karbi Naira miliyan 3 ‘yan fashin sun ki sakin dan uwansa.
Kefas ya bayyana cewa an sanar da rasuwar dan uwansa marigayi a ranar Alhamis.
Ya bayyana cewa a baya ‘yan fashin sun bukaci Naira miliyan 200.
A cewarsa, “Daga baya sun sauka Naira miliyan 5 da babura 3, daga baya suka karbi babur daya. Bayan tattara babur, ba mu sake jin duriyarsu ba. Mun yi ƙoƙarin yin magana da su amma abin takaici, ba mu sami damar ba.
Ya ci gaba da cewa, a lokacin da mai sasantawar ya kira ‘yan bindigar a ranar Alhamis, sai suka ce dan uwansu ya rasu, inda ya ce tun da farko sun dauka cewa barayin na wasa ne amma da suka ci gaba sai ‘yan fashin suka yi barazanar bin sawun wanda ya kira su kuma su zo su same shi idan suka zo. bai daina kiran layinsu ba.
Ya ce ‘yan bindigar sun bayyana cewa sun huce haushin kan dan uwansu ne ta hanyar kashe shi biyo bayan kashe mutanen da ‘yan sanda suka yi.
Ibrahim ya bayyana cewa ‘yan fashin suna neman Naira miliyan 10, domin su gaggauta sakin gawar, ya na mai cewa su (’yan fashi) ba za su yi aiki kyauta ba.
Labarai
Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni
Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.
Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.
Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.
Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.
A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.
Labarai
Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha
Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.
Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.
Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.
“Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”
Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.
Labarai
Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa
An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.
Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.
Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.
-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya2 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su