Connect with us

Manyan Labarai

Zaben 2023: An yi gamo tsakanin Atiku da Tinubu a Abuja

Published

on

‘Yan takarar shugaban kasa biyu na kan gaba a zaben 2023 mai zuwa, Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), da Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP, sun gana a Abuja ranar Litinin a wani bangare na kebantaccen filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja. .

Yayin da Tinubu ke kan hanyarsa ta zuwa garin Jos na jihar Filato, domin kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar APC, Atiku ya na dawowa daga yakin neman zabensa.

Haka kuma akwai shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu da sauran manyan jiga-jigan jam’iyyun biyu.

Kwanakin baya, sansanin Atiku ya yi ta zarge-zarge a kan mai rike da tutar jam’iyyar APC wanda sansanin Tinubu ya yi watsi da shi.

Hangen Dala

Zargin Almundahana:- An kama jami’in gwamnatin Kano

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da kama Tasiu Al’amin-Roba, babban mataimaki na musamman (SSA), ga gwamnan jihar kano da kuma wani Abdulkadir Muhammad bisa zargin su da karkatar da kayan abincin tallafi a jihar Kano.

 

Kwamishinan ‘yan sandan, Hussaini Gumel, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN hakan a wata hira ta wayar tarho a ranar Lahadi cewa, an kama wadanda ake zargin ne a wani dakin ajiyar kaya da ke Sharada dauke da jakunkuna sama da 200.

 

Ya kara da cewa wadanda ake zargin sun yi awon gaba da shinkafa da masara a ma’ajiyar da ke Sharada.

 

“Tun daga lokacin ne muka fara bincike mai zurfi don gano buhunan masara ko shinkafa nawa aka diba aka sayar da su,” inji shi.

 

Gumel ya ce za a gurfanar da mutanen biyu a gaban kotu bayan kammala bincike .

Continue Reading

Hangen Dala

An yiwa kasafin Kudin 2024 karatu na biyu

Published

on

Majalisar Dattawan Najeriya da ta Wakilai sun yi wa kasafin kuɗin ƙasar na 2024 karatu na biyu ranar Juma’a kwana biyu bayan Shugaba Bola Tinubu ya gabatar musu da shi.

A ranar Laraba ne Tinubu ya je majalisar tare da gabatar da naira tiriliyan 27.5 a matsayin kasafin abin da gwamnatinsa za ta kashe a 2024, kuma ya nemi ‘yan majalisar su gaggauta amincewa da shi.

Sai dai shugaban bai bayyana adadin abin da kowace ma’aikata da hukumomin gwamnati za su samu ba a lokacin da ya yi gabatarwar, abin da ya jawo cecekuce da muhawara a ƙasar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito ‘yan majalisar na kokawa yayin muhawarar da suka yi ranar Juma’a game da ƙarancin bayanai kan kasafin, wanda suka ce ya sa sun mayar da hankali ne kawai kan abubuwan da Tinubu ya faɗa a jawabinsa.

Jam’iyyun adawa sun soki kasafin da cewa “na yaudara ne”, yayin da Shugaba Tinubu ya yi masa laƙabi da “kasafin sabunta fata”.

Continue Reading

Manyan Labarai

Hajiya Aisha Bura ta lashe zaben shugaban mata yan jarida na kasa NAWOJ

Published

on

Zaɓaɓɓiyar shugabar kungiyar mata ƴan jarida ta ƙasa Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta alkawarta yin tafiya da kowanne bangare domin samar da hadin kai da ci gaban mambobin kungiyar.

Hajiya Aisha Bura ta bayyana hakan jim kadan bayan kammala rantsar da ita a matsayin wadda ta samu nasarar lashe zaben da aka gudanar a daren jiya.

Ta ce, akwai bukatar mambobin kungiyar su bata hadin kai don ganin ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta.

Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta samu nasara da kuri’u 498 yayin da abokiyar takarar ta kuma shugabar kungiyar mai barin gado Hajiya Ladi Bala ta samu kuri’u 381.


Continue Reading

Trending