Connect with us

Labarai

Martanin DSS game da shugaban hukumar zabe INEC.

Published

on

  • DSS na sane da yadda wasu miyagu ke son tayar da rikici a kasar nan.
  • DSS bata kai karar shugaban INEC kotu ba.

 

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta musanta labarin da ke yawo cewa tana cikin hukumomin tsaron da suka maka Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu a kotu.

Kakakin rundunar, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan a ganawarsa da manema labarai, inda ya yi karin haske kan umarnin wata Babbar Kotun Abuja na hana hukumomin tsaro ciki har da DSS din kama Yakubu.

A ranar Laraba ce dai Alkalin Kotun, M. A. Hassan ya ki amince da bukatar tsige shugaban INEC din daga mukaminsa, saboda zargin kin bayyana ainihin kadarorin da ya mallaka.

Alkalin ya ce kadarorin da Yakubun ya bayyana haka suke, kuma sun yi daidai da tanadin dokokin Najeriya.

Hukuncin dai ya biyo bayan karar da Somadina Uzoabaka ta shigar da Babban Lauyan Gwamnatin da Farfesa Yakubu mai lamba FCT/HC/GAR/CV/47/2022, don tilasta wa shugaban hukumar ta INEC sauka daga matsayinsa, har sai an gudanar da binciken wasu zarge-zargen da hukumomin tsaro daban-daban ke yi masa.

Sai dai Afunanya ya ce kwata-kwata DSS ba ta cikin hukumomin tsaron da suka shigar da waccan karar.

DSS na sane da yadda wasu miyagu ke son tayar da rikici a kasar nan, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.

“Kuma wannan na daya daga cikin dabarun su na yin zagon kasa da lalata kokarinmu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.

“Don haka ina amfani da wannan dama, don wanke DSS da kuma fahimtar da al’umma cewa, ba gaskiya ba ne cewa mun kai karar shugaban INEC kotu”, in ji Kakakin.

 

Labarai

Mun dawo da Alhazan da suka gamu da rashin lafiya yayin aikin hajjin bana – NAHCON

Published

on

Hukumar kula da aikin Hajji ta kasa NAHCON, ta dawo da wasu Alhazan ta na jihohi uku waɗanda suka gamu da rashin lafiya a kasar Saudi Arebia, yau Litinin, sakamakon samun lafiyar da suka yi.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar NAHCON ta ƙasa, Musa Ubandawaki ya fitar a yau Litinin, jim kadan bayan Alhazan sun sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke birnin tarayya Abuja, a ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Malam Jalal Ahmad Arabi.

Ta cikin sanarwar Ubandawaki, ya ce Alhazan jihohin uku da suka gamu da rashin lafiya a kasa mai tsarki, sun haɗar da Muhammad Sulaiman daga jihar Katsina, da Abubakar Sadik daga Kaduna, sai kuma Hajiya Aisha daga jihar Sokoto.

Sanarwar ta ce Alhazan sun gamu da rashin lafiya ne a kasar bayan sun kammala ibadar aikin Hajjin daya gabata na 2024, wanda aka kwantar dasu a Asibiti inda suka samu kulawar likitoci, kuma izuwa yanzu sun warke wanda hakan yasa NAHCON ta dawo dasu gida Najeriya.

Wakilinmu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim ya ruwaito cewa, a aikin hajjin bana an samu yawaitar masu fama da matsalar rashin lafiya, sai dai an alaƙanta rashin lafiyar ne da yadda aka samu zafin rana a ƙasar Saudiyar.

Continue Reading

Labarai

Mun kulle Asibitoci masu zaman kan su 12 a Kano – PHIMA

Published

on

Hukumar da ke kula da Asibitoci masu zaman kan su ta jihar Kano PHIMA, ta ce zata ci gaba da daukar mataki akan dukkanin Asibitocin da suka saɓa ƙa’idar aiki, domin tsaftace harkar tare da samun damar kulawa da marasa lafiya cikin ka’ida.

Shugaban hukumar ta PHIMA, a nan Kano Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Juma’a 05 ga watan Yunin 2024.

Farfesa Salisu Ahmad, ya kuma ce daga zuwan sa hukumar zuwa yanzu aƙalla sun kulle Asibitoci guda 12, kuma akwai uku daga ciki an cire su daga tsarin asibitoci gaba ɗaya bisa sablɓa ka’idar aiki.

“Zamu ɗauki mataki akan dukkanin masu magungunan gargajiyar da suke zagayawa cikin unguwanni suna damun mutane da karar amsa kuwa, ko kuma bayyana batsa ta hanyar tallata magungunan nasu, domin tsaftace harkar, in ji Salisu”.

Wakilinmu Abdulkadir Muhammad Sani Tukuntawa ya rawaito cewa Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ya kara da cewa yanzu haka hukumar ta PHIMA, tayi nisa wajen yiwa masu magungunan gargajiya
rijista tare da tantance su, domin tsarkake harkar da kuma gujewa fuskantar matsala.

Continue Reading

Labarai

Jami’an mu ku gujewa karɓar cin hanci da rashawa yayin aiki – Immigration

Published

on

Shugabar hukumar da ke kula da shige da fice ta kasa Immigration, Kemi Nanna Nandap, ta bukaci jami’ansu da su kaucewa karbar cin hanci da Rashawa a iyakokin kasa, tare da aiki tuƙuru yayin da suke gudanar da ayyukansu a iyakokin Najeriya.

Shugabar Kemi Nanna, da ta samu wakilcin HK Usman, yayin taron da hukumar kula da shige da ficen reshen jihar Kano Immigration, ta gudanar yau a hedikwatar ta, inda ta kaddamar da yaki da cin hanci da rashawa a tsakanin jami’an hukumar da kuma al’umma.

Ta kuma ce kaddamar da al’amarin zai taimaka wajen daƙile cin hanci da
rashawa a tsakanin jami’an su da kuma al’umma musamman ma a iyakokin kasar nan da kuma ofisoshin da suke aiki.

“Nasan mu masu tsaron ƙasa ne musamman ma a iyakokin ƙasa, dole ne mu yi abinda ya kamata wajen daƙile cin hanci da rashawa a cikin aikin mu: kuma jami’an mu idan suka yi aiki tuƙuru za’a samu nasara, “in ji shi”.

Da yake nasa jawabin shugaban hukumar kula da shige da fice Immigration, ta kasa reshen jihar Kano, Ibrahim Muhammad Abubakar, ya ce sun shirya taron ne domin ƙaddamar da kawar da cin hanci da rashawa a cikin aikin nasu, kasancewar ba abu ne mai kyau ba.

Ya kuma nemi goyon bayan al’ummar ƙasar nan wajen magance harkokin cin hanci da rashawa, musamman ma tsakanin su da jami’an hukumar.

Wakilin Dala FM Kano, Hassan Mamuda Ya’u ya ruwaito cewa taron ya samu halartar jami’an hukumar da dama ciki har na birnin tarayya Abuja, da kuma jami’an tsaro, kuma ciki har da jami’an hukumar kula da gidan gyaran hali na jihar Kano, da na rundunar tsaro ta Civil Defense, da kuma hukumomin gwamnati da dai sauran su.

Continue Reading

Trending