Connect with us

Manyan Labarai

Wanda bashi da asusun banki ya bude -CBN

Published

on

Bankin kasa

CBN ya shawarci Al’ummar Najeriya da su bude asusun banki

  • Yan kasa da suke kauyuka su gaggauta fitar da kudadensu zuwa banki cewar CBN
  • wa’adin da CBN ya bayar na karban tsoffin kudi ya kusa cika
  • Babban bankin ƙasa CBN ya shawarci yan Nigeria marasa asusun banki da su  bude, domin ajiye tsoffin kuɗaɗen kafin 31 ga watan Janairu da muke ciki.

Shafin matambayi baya bata ya bayyana cewa Babban bankin yayi kira ga ƴan ƙasa da suke zaune a ƙauyuka da su gaggauta fitar da kuɗaɗen da suke ajiye dasu domin a sauya musu, an kuma basu damar ziyartar kowane banki dake kusa dasu domin buɗe asusun.

CBN ya haramta bayar da sabbin kudi akan kanta

CBN yace a rahotannin da suke samu har yanzu tsoffin kuɗi ne suke yawo a tsakanin Al’umma, yana mai cewa nan ba da daɗewa kuɗaɗen zasu karaɗe ko ina.

Manyan Labarai

Gawuna ya taya Abba Gida Gida murna

Published

on

Dan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a zaben 2023 Dakta Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana karbar kaddara tun bayan da ya Fadi zaben 18 ga watan Maris.

Cikin Wani Sakon murya, Dakta Nasiru Gawuna ya godewa magoya baya, tare da yin fatan alkhairi ga sabuwar gwamnati.

” Wannan sabuwar gwamnati Allah ya Bata ikon yiwa al’umma adalchi, mu Kuma Allah ya bamu ikon yin biyayya.”

 

 

Continue Reading

Manyan Labarai

Abba Gida Gida ya karbi shaidar lashe zabe

Published

on

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida gida ya karbi shaidar lashe zaben Gwamnan Kano.

Ya karbi wannan shaida ce yayin wani taro da hukumar INEC ta shirya domin bashi shaidar satifiket, bayan nasarar da ya samu a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.

Taron dai Wanda ya samu halartar da dama daga cikin manyan jihar Kano dama shiyyar arewa maso yamma, ya gudana ne a dakin taro na ofishin hukumar zabe INEC na jihar Kano.

Continue Reading

Labarai

Marayu na buƙatar tallafi sosai – Kwamared Abu Saleem

Published

on

Shugaban ƙungiyar tallafawa Marayu da ci gaban al’umma ta ƙaramar hukumar Birnin Kano Kwamared Adam Umar Abu Saleem, ya ce ƙarancin samun tallafi daga masu ƙarfi ne ke sanyawa Marayu ke faɗawa cikin mawuyacin hali.

Kwamared Adam Abu Saleem na wannan jawabin ne yayin zantawarsa da gidan rediyon Dala FM, lokacin musabaƙar Alƙur’ani mai girma na marayu ƴan ƙaramar hukumar Birni 5 yayin da ɗalibi dake Karkasara Ja’afar Aliyu Abubakar ya zama gwarzon shekara na ƙaramar hukumar wanda aka ɗauki nauyin al’amuran rayuwarsa baya ga kyaututtuka da ya samu, wanda Musabaƙar ta gudana cikin Firamen Salanta a ranar Asabar.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa Kwamared Adam ya ce sukan shirya Musaɓakar ne domin zaburar da Marayu akan harkokin karatun Alkur’ani mai girma, da kuma rage musu wani tunanin maraici da suke kasancewa a maban-banta lokuta.

Continue Reading

Trending