Connect with us

Manyan Labarai

Na sauke nauyin da ‘yan Nigeria suka dora min – Buhari

Published

on

Shugaba Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya mulki Najeriya da iyakar ƙokarinsa, inda ya ce bai ba wa ‘yan ƙasar kunya ba.

Shugaban wanda ya je jihar Bauchi a cigaba da ƴaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC na shugaban ƙasa da kuma na gwamna, ya bayyana hakane lokacin da ya kai ziyara gidan Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman Adamu.

Buhari ya ce dubban mutane da suke fitowa su tarbe shi a duk inda ya je hakan na nuna ƙarara irin soyayyar da ake masa.

Ina so na faɗa cewa tsakanin 2003 zuwa 2011, na kai ziyara dukkanin ƙananan hukumomin Najeriya, sannan a 2019, lokacin da nake neman sake komawa kan mulki ƙaro na biyu, na ziyarci dukkanin jihohi a faɗin ƙasar, mutanen da naga sun fito tarba ta, abu ne da ba zan iya misaltawa ba saboda dandazonsu, a lokacin na yi alkawarin mulkar Najeriya da ‘yan Najeriya da iyaƙar ƙokarina kuma zuwa yanzu na san na yi ƙokari,” in ji shugaban.

Tun da farko a jawabinsa, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman, ya ce abu mai kyau ne idan shugabannin siyasa suka nuna girmamawa ga Sarakuna da kuma masarautu ta hanyar kai musu ziyara.

Ya godewa shugaba Buhari kan irin ci gaban da gwamnatinsa ta kawo a Bauchi, inda ya ce aikin haƙo man fetur na Kolmani, wani bu ne da ‘yan jihar da ma arewa maso gabas ba za su manta ba.

Baba Suda

Gwamnatin Kano ta musanta labarin da ke cewa za ta saka kafar Wando daya da Sojojin Baka

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta musanta labarin da ke yawo na cewa za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishinan yada labaran jihar Kwamred Ibrahim Waiya shi ne ya bayyana hakan lokacin wani taron karawa juna sani da hukumar kula da kafafen yada labarai NBC ta shirya a yau Alhamis.

 

Yace gwamnatin Kano za ta hada kai da Yan siyasa masu magana a Rediyo da aka fi Sani da Sojojin Baka, domin tsaftace harkokin siyasar Kano.

 

Haka kuma kwamishinan ya musanta labarin da ke cewa Gwamnatin Kano za ta saka kafar wando daya da Sojojin Baka.

 

Kwamishina Waiya ya kuma ce za su hada kai da kafafen yada labarai domin Kara kawo tsafta a harkokin siyasar Kano.

Continue Reading

Manyan Labarai

Da Ɗumi-Ɗumi! Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakin sa da ƴan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani taƙaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin ƴan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan, tare da sanya dokar ta ɓaci a jihar.

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya daɗe da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saƙa tsakanin sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Continue Reading

Manyan Labarai

Isra’ila ta kashe sama da mutane 200 bayan karya yarjejeniyar tsagaita Wuta a Gaza

Published

on

Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, tare da ƙaddamar da sabbin hare-hare kan Falasdinawa.

Jaridar TRT Hausa ta ruwaito cewa, aƙalla Isra’ila ta kashe fiye da mutum 200 tare da jikkata ɗaruruwa a yayin da ake ci gaba da kai gawawwaki asibiti, kamar yadda majiyoyin wani asibiti a yankin Gaza suka bayyana.

Continue Reading

Trending