Connect with us

Manyan Labarai

Hukumar Neco ta saki sakamakon jarrabawa

Published

on

Daliban Neco

Hukumar shirya jarrabawar kasa, NECO, ta fitar da sakamakon jarrabawar da aka yi ta watan Nuwamba da Disamba na 2022 ta daliban manyan makarantun sakandire.

Shugaban hukumar Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, shi ne ya bayyana hakan a Minna, babban birnin jihar Niger.

A bayanin da ya yi, ya ce a jumullar dalibai 59,124 da suka yi jarrabawar, daga cikinsu 31,316 maza ne waɗanda yawansu shi ne kashi 52.96 cikin ɗari.

Yayin da mata suka kasance 27,808, kashi 47.03 cikin ɗari.

Da Duminsa: An saki sakamakon jarabawar NECO

Hukumar ta NECO, wadda ta fitar da sakamakon jarrabawar bayan kwana 57, ta kuma ce an samu dalibai 11,419 da laiffukan da suka danganci satar jarrabawa, saɓanin 4,454 da aka kama 2021, wanda hakan ta ce ya nuna ƙaruwar matsalar sosai.

Labarai

Mu yawaita karanta Alƙur’ani da aikin alkhairi a watan Ramadan – Malam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallaacin Juma’a na Salafussalih dake unguwar Ɗorayi ƙarama Malam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’ummar musulmi da su ƙara himma wajen karanta Al-ƙur’ani mai girma, tare da aikata ayyukan alkhairi domin rabauta da rahamar Allah S.W.T a nan duniya dama gobe ƙiyama.

Mallam Ibrahim Bunkure ya bayyana hakan ne lokacin da yake tsokaci kan huɗubar Juma’ar da ya gabatar yau a masallacin.

Ya ce, kamata yayi musulmai su ƙara yin koyi da kyawawan ɗabi’un Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama, domin zama ababen koyi a rayuwa.

Wakilinmu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewar Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya kuma shawarci al’umma da su ƙara kasancewa masu yafiya musamman a lokacin da aka yi mutu abinda bai musu daɗi ba, bisa mahimmancin da hakan yake da shi.

Continue Reading

Manyan Labarai

Gawuna ya taya Abba Gida Gida murna

Published

on

Dan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a zaben 2023 Dakta Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana karbar kaddara tun bayan da ya Fadi zaben 18 ga watan Maris.

Cikin Wani Sakon murya, Dakta Nasiru Gawuna ya godewa magoya baya, tare da yin fatan alkhairi ga sabuwar gwamnati.

” Wannan sabuwar gwamnati Allah ya Bata ikon yiwa al’umma adalchi, mu Kuma Allah ya bamu ikon yin biyayya.”

 

 

Continue Reading

Manyan Labarai

Abba Gida Gida ya karbi shaidar lashe zabe

Published

on

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida gida ya karbi shaidar lashe zaben Gwamnan Kano.

Ya karbi wannan shaida ce yayin wani taro da hukumar INEC ta shirya domin bashi shaidar satifiket, bayan nasarar da ya samu a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.

Taron dai Wanda ya samu halartar da dama daga cikin manyan jihar Kano dama shiyyar arewa maso yamma, ya gudana ne a dakin taro na ofishin hukumar zabe INEC na jihar Kano.

Continue Reading

Trending