Manyan Labarai
Jerin ma’aikatun Ministocin Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya baiwa Mutum 45 cikin 47 da majalisar dattawa ta tantance kuma ta tabbatar a matsayin ministoci maaikatun su.
Ga jerin sunayen ministcoin da ma’aikatunsu:
Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Dijita – Bosun Tijani
Ƙaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco
Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki – Wale Edun
Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji
Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu
Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa
Ministan Ma’adanai – Dele Alake
Ministan Yawon Buɗe-Ido – Lola Ade-John
Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola
Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite
Ministan Wasanni – John Enoh
Ministan Abuja – Nyesom Wike
Ministar Al’adu – Hannatu Musawa
Ministan Tsaro – Muhammad Badaru
Ƙaramin Ministan Tsaro – Bello Matawalle
Ƙaramin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sununu
Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Ahmed M. Dangiwa
Ƙaramin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Abdullah T. Gwarzo
Ministan Kasafi da Tsare-Tsare – Atiku Bagudu
Ministan Muhalli (Kaduna)
Ƙaramar Ministar Abuja – Mairiga Mahmud
Ministan Albarkatun Ruwa – Bello M. Goronyo
Ministan Noma da Samar da Abinci – Abubakar Kyari
Ministan Ilimi – Tahir Maman
Ministan Harkokin Cikin Gida – Sa’Idu A. Alkali
Ministan Harkokin Waje – Yusuf M. Tuggar
Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a – Ali Pate
Ministan Harkokin ‘Yan Sanda – Ibrahim Geidam
Ƙaramin Ministan Ƙarafa – U. Maigari Ahmadu
Ministan Ƙarafa – Shuaibu A. Audu
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai – Muhammed Idris
Ministan shari’a – Lateef Fagbemi
Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Simon B. Lalong
Ƙaramar Ministar Harkokin Cikin Gida – Imaan Sulaiman-Ibrahim
Ministan Ayyuka na Musamman – Zephaniah Jisalo
Ministan Albarkatun Ruwa – Joseph Utsev
Ƙaramin Ministan Noma da Samar da Abinci – Aliyu Sabi Abdullahi
Ministan Kimiyya da Fasaha – Uche Nnaji
Ƙaramar Ministar Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Nkiruka Onyejeocha
Ministar Harkokin Mata – Uju Kennedy
Ministan Ayyuka – David Umahi
Ministan Sufurin Jiragen Sama – Festus Keyamo
Ministan Matasa – Abubakar Momoh
Ministar Agajin Gaggawa da Rage Talauci – Betta Edu
Ƙaramin Ministan Albarkatun Iskar Gas -Ekperikpe Ekpo
Ƙaramin Ministan Man Fetur – Heineken Lokpobiri.
Za dai a rantsar dasu ne a ranar 21 ga watan Agustan da muke ciki a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Manyan Labarai
Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.
Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.
Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.
A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.
Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Manyan Labarai
Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.
Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.
“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.
Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.
Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.
Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.
Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Manyan Labarai
Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.
Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a
“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.
Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.
Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

-
Nishadi5 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai4 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi5 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi5 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su