Connect with us

Manyan Labarai

Jerin ma’aikatun Ministocin Tinubu

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya baiwa Mutum 45 cikin 47 da majalisar dattawa ta tantance kuma ta tabbatar a matsayin ministoci maaikatun su.

 

Ga jerin sunayen ministcoin da ma’aikatunsu:

 

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Dijita – Bosun Tijani

Ƙaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco

Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki – Wale Edun

Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji

Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu

Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa

Ministan Ma’adanai – Dele Alake

Ministan Yawon Buɗe-Ido – Lola Ade-John

Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola

Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite

Ministan Wasanni – John Enoh

Ministan Abuja – Nyesom Wike

Ministar Al’adu – Hannatu Musawa

Ministan Tsaro – Muhammad Badaru

Ƙaramin Ministan Tsaro – Bello Matawalle

Ƙaramin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sununu

Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Ahmed M. Dangiwa

Ƙaramin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Abdullah T. Gwarzo

Ministan Kasafi da Tsare-Tsare – Atiku Bagudu

Ministan Muhalli (Kaduna)

Ƙaramar Ministar Abuja – Mairiga Mahmud

Ministan Albarkatun Ruwa – Bello M. Goronyo

Ministan Noma da Samar da Abinci – Abubakar Kyari

Ministan Ilimi – Tahir Maman

Ministan Harkokin Cikin Gida – Sa’Idu A. Alkali

Ministan Harkokin Waje – Yusuf M. Tuggar

Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a – Ali Pate

Ministan Harkokin ‘Yan Sanda – Ibrahim Geidam

Ƙaramin Ministan Ƙarafa – U. Maigari Ahmadu

Ministan Ƙarafa – Shuaibu A. Audu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai – Muhammed Idris

Ministan shari’a – Lateef Fagbemi

Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Simon B. Lalong

Ƙaramar Ministar Harkokin Cikin Gida – Imaan Sulaiman-Ibrahim

Ministan Ayyuka na Musamman – Zephaniah Jisalo

Ministan Albarkatun Ruwa – Joseph Utsev

Ƙaramin Ministan Noma da Samar da Abinci – Aliyu Sabi Abdullahi

Ministan Kimiyya da Fasaha – Uche Nnaji

Ƙaramar Ministar Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Nkiruka Onyejeocha

Ministar Harkokin Mata – Uju Kennedy

Ministan Ayyuka – David Umahi

Ministan Sufurin Jiragen Sama – Festus Keyamo

Ministan Matasa – Abubakar Momoh

Ministar Agajin Gaggawa da Rage Talauci – Betta Edu

Ƙaramin Ministan Albarkatun Iskar Gas -Ekperikpe Ekpo

Ƙaramin Ministan Man Fetur – Heineken Lokpobiri.

Za dai a rantsar dasu ne a ranar 21 ga watan Agustan da muke ciki a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Manyan Labarai

Fadan dabar kofar Na’isa da kofar Dan-agundi, laifin iyaye – Mazaunin Yankin

Published

on

Wani mazaunin ƙofar Na’isa wanda ya buƙaci a sakaye sunansa, ya ce faɗan dabar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a yankin da Ɗan Agundi, laifin iyaye ne, da kuma wasu manya a unguwannin da ake zargin suna goya musu baya ta hanyar daƙile yunƙurin hukumomi na ɗaukar doka a kansu.

Mutumin ya bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, biyo bayan yadda rikicin faɗan dabar ya sake ɓarkewa a unguwannin a Alhamis ɗin nan, al’amarin da ya janyo asarar dukiyoyin al’umma a yankunan.

Ya ce lamarin ya faro ne tun a lokacin bikin ƙaramar Sallah, lamarin da a baya ƙura ta lafa, sai dai kuma a ranar Alhamis ɗin sai gashi an sake samun faɗan dabar.

A cewar sa, “A lokacin faɗan dabar ya faru an Sassari mutane da dama, hatta Saniya ma ba ta tsira ba sai da aka sareta, tare da fasa gilasan ababen hawan Mutane, “in ji shi”.

Sa dai mutumin ya ce, tuni jami’an tsaron Ƴan Sanda, suka kai ɗauki tare da kwantar da tarzoma, lamarin da ƙurar ta lafa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ba za mu amince da yadda ake yawan kai wa jami’an mu hari ba a Kano – KAROTA

Published

on

Hukumar kula da zirgar-zirgar ababen Hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce ba za ta lamunta da yadda ake yawan kai wa jami’anta farmaki ba, na ba gaira babu dalili yayin da suke gudanar da ayyukan su.

Shugaban Hukumar KAROTA, a Kano, Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya yi wannan gargaɗin ta cikin sanarwar da kakakin hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya aikowa tashar Dala FM Kano, a ranar Laraba 09 ga watan Afrilun 2025.

“Hakan na zuwa ne biyo bayan wani mummunan hari da wasu mutane da ke cikin baburin Adai-daita sahu suka kai wa jami’an na mu yayin da suke tsaka da aikinsu a titin da ke dab da gidan Buhari kan hanyar zuwa Gidan Zoo, “in ji shi“.

Sanarwar ta ce, tunda farko an tsayar da wani mai baburin Adai-daita Sahu ne inda yaƙi tsayawa, sai kawai aka hango mai ɗan sahun ya naushi jami’in karotar.

Sai dai a ta bakin Shugaban kungiyar ‘Yan Adai-daita Sahu a jihar Kano, ya ce waɗannan mutane ba halattattun ‘Yan Adai-daita Sahu ba ne, sun dai fake da sana’ar su dan aikata ta’addanci.

Daga bisani dai jami’n hulɗa da jama’a na Hukumar Koratar, Abubakar Ibrahim Sharada, ya ce hukumar za ta ɗauki tsattsauran mataki akan lamarin, don kare afkuwar irin hakan a gaba.

Hukumar ta ce duk wanda ya ga faruwar wani abu da ya shafe ta, ko kuma ƙorafe-ƙorafe, zai iya kiran waɗannan lambobin domin sanar da ita, da suka haɗar da 09015709449 ko 08059689422 ko kuma 08067311520.

Continue Reading

Manyan Labarai

Ɗan Bijilante ya rasa ransa bisa arangamar su da wasu ƴan Daba a Kano

Published

on

Ƙungiyar sintirin Bijilante ta ƙasa reshen jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin kwamandan ta Ubale Barau Muhammad Badawa, ta tabbatar da rasuwar guda daga cikin jami’in ta mai suna Suraj Rabi’u mazaunin Jaba da ke ƙaramar hukumar Fagge a jihar, sakamakon arangama da ƴan Daba.

Mai magana da yawun ƙungiyar Bijilante na jihar Kano, kuma Kwamandan ta na ƙaramar hukumar Fagge, Usman Muhammad Ɗan Daji, shi ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikowa Dala FM Kano a ranar Lahadi.a

“Jami’in Bijilanten namu ya rasa ran nasa ne sakamakon arangama da suka yi da wasu Ƴan Daba yayin gudanar aikinsu a ranar Idin ƙaramar Sallah, inda ƴan dabar suka soke shi da Ɗanbida a Ƙirji da bayansa, wanda ya yi sanadiyar rasuwarsa, “in ji Usman”.

Ya kuma ce, an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi mai suna Usman Sharif mazaunin ƙaramar hukumar Dala, kuma tuni aka miƙa shi hannun jami’an tsaro.

Usman Ɗan daji, ya kuma yi addu’ar Allah ya jiƙan jami’in nasu ya gafarta masa.

Continue Reading

Trending