Manyan Labarai
Jerin ma’aikatun Ministocin Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya baiwa Mutum 45 cikin 47 da majalisar dattawa ta tantance kuma ta tabbatar a matsayin ministoci maaikatun su.
Ga jerin sunayen ministcoin da ma’aikatunsu:
Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Dijita – Bosun Tijani
Ƙaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco
Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki – Wale Edun
Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji
Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu
Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa
Ministan Ma’adanai – Dele Alake
Ministan Yawon Buɗe-Ido – Lola Ade-John
Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola
Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite
Ministan Wasanni – John Enoh
Ministan Abuja – Nyesom Wike
Ministar Al’adu – Hannatu Musawa
Ministan Tsaro – Muhammad Badaru
Ƙaramin Ministan Tsaro – Bello Matawalle
Ƙaramin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sununu
Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Ahmed M. Dangiwa
Ƙaramin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Abdullah T. Gwarzo
Ministan Kasafi da Tsare-Tsare – Atiku Bagudu
Ministan Muhalli (Kaduna)
Ƙaramar Ministar Abuja – Mairiga Mahmud
Ministan Albarkatun Ruwa – Bello M. Goronyo
Ministan Noma da Samar da Abinci – Abubakar Kyari
Ministan Ilimi – Tahir Maman
Ministan Harkokin Cikin Gida – Sa’Idu A. Alkali
Ministan Harkokin Waje – Yusuf M. Tuggar
Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a – Ali Pate
Ministan Harkokin ‘Yan Sanda – Ibrahim Geidam
Ƙaramin Ministan Ƙarafa – U. Maigari Ahmadu
Ministan Ƙarafa – Shuaibu A. Audu
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai – Muhammed Idris
Ministan shari’a – Lateef Fagbemi
Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Simon B. Lalong
Ƙaramar Ministar Harkokin Cikin Gida – Imaan Sulaiman-Ibrahim
Ministan Ayyuka na Musamman – Zephaniah Jisalo
Ministan Albarkatun Ruwa – Joseph Utsev
Ƙaramin Ministan Noma da Samar da Abinci – Aliyu Sabi Abdullahi
Ministan Kimiyya da Fasaha – Uche Nnaji
Ƙaramar Ministar Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Nkiruka Onyejeocha
Ministar Harkokin Mata – Uju Kennedy
Ministan Ayyuka – David Umahi
Ministan Sufurin Jiragen Sama – Festus Keyamo
Ministan Matasa – Abubakar Momoh
Ministar Agajin Gaggawa da Rage Talauci – Betta Edu
Ƙaramin Ministan Albarkatun Iskar Gas -Ekperikpe Ekpo
Ƙaramin Ministan Man Fetur – Heineken Lokpobiri.
Za dai a rantsar dasu ne a ranar 21 ga watan Agustan da muke ciki a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Hangen Dala
Jami’ar Chikago ta baiwa Atiku bayanan Tinubu

Jami’ar Jihar Chicago da ke Amurka ta saki takardun karatun Shugaba Bola Tinubu, bayan da ɗan takarar shugaban ƙasar a a 2023 ƙarƙashin jam’iyyar PDP Atiku Abubukar ya buƙaci hakan.
A ƙarshen makon da ya gabata ne, wata kotun gunduma da ke arewacin Illinois a Amurka ta bayar da umarnin a sakarwa Atiku takardun karatun Tinubu.
A wani martani na buƙatar da Atiku ya miƙa a karo na uku, wanda ya nemi a saki kwafin sakamakon digiri 1977, Jami’ar ta ce takardun sun yi daidai da na Tinubu da ke ɗauke da kwanan watan 27 ga watan Yunin 1977.
“Bayan bincike mai zurfi, Jami’ar CSU ta gano ta kuma gabatar da takardun da aka nema kuma ta gabatar da su don amsa wannan bukatar. Lambobin takardun su CSUO008 zuwa CSU0010.
“An shafe sunayen ɗaliban da ke kan takardun saboda a sakaya sunansu.
“CSU za ta kuma saki sakamakon daliban da suke kusa da shi, masu lamba CSU0011 da lamba 0017 na wasu ɗaliban bayan an doɗe sunayen (saboda a sakaye sunanyensu)”.
“Waɗannan takardun sun yi daidai da yadda na Tinubu, dalibin da aka yi wa sauyin makaranta yake,” kamar yadda jami’ar ta rubuta.
A baya Tinubu ya yi iƙirarin ɓatan ainihin takardunsa na jami’ar, abin da ya sa ya gabatarwa da hukumar zaɓe INEC wata takardar a matsayin madadin takardun na ainihi domin takarar shugabancin Najeriya a 2023.
Takardu da dama na waɗari a kafafen sada zumunta a matsayin shaidar kammala karatun na Tinubu a Jami’ar jihar Chicago.
Tambari da kuma bajon da jami’ar CSU ta saki na digirin a 1977 sun yi daidai da irin wanda Shugaba Tinubu ya gabatar wa INEC, sai dai an samu banbanci a kwanan wata.
Sai dai cikin bayanin da jami’ar ta yi, ta ɗauki alhakin kuskuren da aka samu a kwanan watan, tana cewa kuskure aka samu wajen rubutawa.
A ranar 19 ga watan Satumba ne, Jeffrey Gilbert na kotun majitare da ke Amurka ya amince da buƙatar da aka shigabar gaban kotun tare da ba da umarnin sakin takardun karatun Bola Tinubu cikin sa’a 24.
A wani ƙoƙari na ganin haka bai faru ba, Tinubu ya ɗaukaka ƙara kan wannan umarni.
Nancy Maldonado ta kotun tarayya ta sake tabbatar da wannan hukunci da Tinubu ya so ƙalubalanta, inda ita ma ta ce a saki takardun.
Domin bin umarnin kotun da cika buƙatar Atiku Abubakar CSU ta ce ba za ta iya nemo ainihin kwafin takardun da ta bai wa Tinubu ba 1979.
“A tsarin CSU ba ta ajiye kwafin takardun ɗaliban da suka yi digiri, kuma bayan dogon bincike ta gaza samo kwafin irin wanda ta bau wa Tinubu a 1979, don haka ba a samu takardun da aka buƙata ba,” in ji jami’ar.
Sai dai jami’ar ta saki takardun wasu ɗaliban da ta rufe sunayensu, waɗanda suka yi daidai da na Tinubu domin tabbatar da cewa ya kammala makarantar a baya.
Atiku Abubakar dai na son amfani da takardun ne a matsayin shaida a kotun ƙolin Najeriya kan ƙorafin da ya shigar game da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar da aka yi a 2023.
BBC

Manyan Labarai
Shekaru 63 na Nigeria:- Jawabin Gwamnan Kano

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya buƙaci shugabanni da saura al’umma da suyi koyi da tsaffin shugabannin da suka gabata wajen kawowa ƙasar nan ci gaba da zaman lafiya musamman a irin wannan lokaci.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yau yayin da yake jawabi kan cikar ƙasar nan shekara 63 da samun kyancin kai daga hannun turawan mulkin mallaka.
Gwamna Abba ya kuma ce la’akari da yadda ake tunawa da tsaffin shugabanni wajen ciyar da ƙasar nan gaba ya kamata su shugabannin yanzu suyi koyi da su.
Ka zalika ya ƙara da cewa ya kamata shugaban ni su tabbata sun yiwa al’umma abin da suke buƙata domin tabbatar adalci.
Gwamnatin tace zata ci gaba da gudanar da aikin ta kamar yadda ta tsara domin ciyar da Kano gaba.

Hangen Dala
Hukuncin Kaduna :- PDP za ta daukaka kara

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kaduna ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ta tabbatar da zaben Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC, inda ta ce za ta garzaya kotun daukaka kara.
Alberah Catoh, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a a Kaduna.
Catoh ya ce, wani nazari da lauyan PDP ya yi ya nuna cewa hukuncin bai cika wasu ka’idoji na tabbatar adalci ba.
Martanin ya zo ne sa’o’i bayan kotun da ke zamanta a Kaduna ta amince da nasarar zaben Sani.
Ya kara da cewa hukuncin bai dace da wasu dokoki da ka’idojin zabe ba.
Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda haka jam’iyyar ta umurci lauyoyinta da su daukaka kara kan hukuncin da aka yanke a kotun daukaka kara da ke Abuja a cikin wa’adin da doka ta kayyade.”
Catoh ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar PDP a fadin jihar da su kwantar da hankalinsu tare da nuna kwarin gwiwarsu kan lamarin.

-
Nishadi4 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Manyan Labarai4 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai3 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi4 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Labarai4 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya1 year ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Nishadi4 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su
-
Manyan Labarai4 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano