Connect with us

Labarai

Zargin Almundahana:- Gwamnan Kano ya dakatar da manajan Daraktan KASCO

Published

on

Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf na ya bayar da umarnin dakatar da Manajan Daraktan Kamfanin Samar da kayayyakin aikin gona na Kano (KASCO) Dakta Tukur Dayyabu Minjibir.

 

Cikin sanarwar da sakataren yada yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, Gwamnan ya bayar da umarnin dakatarwar ne a wata mai sanarwa mai kwanan wata 12 ga Satumba, 2023 wanda sakataren gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya mika.

 

An dakatar da Manajan Darakta ne bisa zarginsa da hannu a sayar da hatsi mallakin gwamnatin jihar Kano.

 

Gwamnan ya kuma bayar da umurnin gudanar da binciken gaggawa yayin tare da nanata alkawarinsa na kin saurarawa duk wanda aka samu da cin hanci da rashawa.

 

An Kuma umurci Dakta Dayyabu da ya mika al’amuran kamfanin ga babban jami’i a Hukumar nan take har sai an kammala bincike.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending