Connect with us

Manyan Labarai

Muna Allah wa-dai da tsare yaran da gwamnatin tarayya ta kama yayin zanga-zangar tsadar rayuwa  – Human Right

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Global Community for Human Right Network, ta yi Allah wa-dai da matakin gabatar da matasa da yaran nan a gaban kotun tarayya da ke Abuja, waɗanda aka kama a yayin zanga-zangar tsadar rayuwa, a Kano, da Jos da Kaduna.

Gwamnatin tarayya dai tana zargin waɗanda aka kama ɗin ne da zargin cin amanar ƙasa, bayan da take zargin an same su suna ɗaga tutocin ƙasar Rasha a zanga-zangar kawo ƙarshen yunwa da aka gudanar a tsakanin 1 zuwa goma ga watan Agustan 2024.

Shugaban gudanarwar ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ɗin Kwamared Tasi’u Idris Idris (Soja) ya shaidawa Dala FM Kano cewar, babu adalci a gabatar da matasan a gaban kotun, kasancewar mafi yawancin su ƙananan yara ne har da ƴan shekaru 14, da 15, da kuma ƴan shekaru 18.

Tasi’u Soja, ya kuma ce tsare yaran da aka yi kusan watanni uku babu adalci a cikin lamarin, yana mai cewa za su yi duk mai yiyuwa don ganin an yiwa yaran adalci.

“Muna kira ga Ƴan Majalisun Arewa, da Sarakuna, da Ƴan Siyasar Arewa da su yi gaggawar ganawa da fadar shugaban ƙasa domin sakin yaran nan duba da take musu haƙƙi da aka yi, “in ji Tasi’u”.

Rahotanni sun bayyana cewar ana tsaka da shari’ar yaran ne a ranar Juma’a 01 ga watan Nuwamban 2024, sai hudu daga cikin su suka faɗi magashiyyan lamarin da mai shari’ar Oboira Egwyatu ya dakatar da shari’ar don duba yaran.

Kotun dai ta sanya yaran a hannu belin ajiye Naira Miliyan goma-goma kowannen su, tare da wanda zai tsayawa kowannen su mai matakin albashi 15, lamarin da ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ɗin ta ƙalubalanci sharuɗan belin kasancewar ya yi tsauri da yawa tare da rashin adalci a ciki.

A nasa ɓangaren shugaban ƙungiyar iyayen yaran da aka gabatar a gaban kotun tarayya da ke Abuja, Nura Ahmad Muhammad, ya ce talaucin iyayen yaran da kuma rashin kishin ƴan siyasa da masu fada a ji ne yasa ake tuhumar yaransu da laifukan da basu aikata ba.

Manyan Labarai

Mun shirya ɗaukar mataki a kan ƴan siyasar da ke ɗaukar nauyin Ƴan Daba a Kano – Anti-Phone Snaching

Published

on

Rundunar Tsaro da ke yaki da fadan Daba da fashi da makamin Waya da kuma dakile Shaye-shayen kayan maye ta Anti-Phone Snaching, a jihar Kano, ta ce ta gano cewar yadda wasu daga cikin ‘Yan Siyasa ke daukar nauyin ‘Yan Daba na daga cikin daga cikin dalilan da ke kara ta’azzarar ayyukan ‘yan daban a sassan jihar.

Kwamandan rundunar a Kano Inuwa Salisu Sharada ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Litinin, ya ce yanzu haka sun fara bibiya tare da bincike akan irin matasan da suke damun jama’a da fadan Daba a sassan jihar Kano, don gano ‘Yan siyasar da ke da hannu akan lamarin tare da daukar mataki na gaba.

“Abin takaici ne yadda mafi yawancin masu fadan daban ake samun su kananan yara da ba su wuce shekaru 15 zuwa kasa ba, kuma duk da hakan duk wanda mu ka kama ba za mu saurara masa ba, a don haka ne ma mu ke kira ga iyaye da su tsawatar wa ya’yansu, in ji Inuwa”.

A cewar sa, idan suka kama masu harkar faɗan Daba, mafi yawancin su suna kama faɗin wasu daga cikin ƴan siyasa da suke ɗaukar nauyin su, kuma yanzu haka sun dukufa don gano bakin zaren tare da ɗaukar matakin da ya dace akan dukkan masu hannu kan lamarin.

Tuni dai kwamishinan ‘Yan sandan jihar Kano Ibrahim Adamu Bakori, ya kaddamar da sabbin dabarun magance harkokin Daba da fashin Waya da kuma shaye-shayen kayan maye a sassan jihar, bayan da ya gana da manyan jami’an ‘yan sandan a ranar Asabar din da ta gabata.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴan sandan Kano ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile Daba da Fashin Waya a jihar

Published

on

Rundunar Ƴan sandan jihar Kano ta sha alwashin kakkaɓe matsalar faɗab Daba, da fashin waya da makami, da Shaye-shayen kayan maye, da ke addabar jama’a a birnin jihar, don wanzar da zaman lafiya.

Kakakin rundunar ƴan Sandan jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da ya aikewa manema labarai tashar Dala FM ta samu a ranar Lahadi 15 ga watan Yunin 2025.

Kiyawa, ya ce hakan na zuwa ne bayan da kwamishinan ƴan sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ƙaddamar da sabbin matakan daƙile ayyukan ’yan daba da masu fashin waya da makami a birnin Kano da kewaye.

Sanarwar ta bayyana cewa kwamishinan ya gana da manyan jami’an rundunar ne a ranar Asabar 14 ga watan Yunin 2025, inda ya umarce su da su soma sumame a dukkan maɓoyar Ƴan Daba, tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma domin ganin an cafko duk masu hannu a tashe-tashen hankula a faɗin jihar.

“A umarnin da kwamishinan ya bayar, ya umarci dukkanin Baturen Ƴan Sanda wato DPO’s, da shugabannin shiyya na Ƴan Sanda, da sauran dakarun Ƴan sanda, da su nemi haɗin kai da al’umma, tare da ƙara faɗaɗa sintiri don magance matsalolin Daba, da fashin Waya a Kano, in ji Kiyawa”

Har ila yau, rundunar ƴan sandan ta kuma buƙaci haɗin kan jama’a da su rika bayar da bayanan sirri a kan yan daban, ta hanyar kiran waɗannan lambobin wayar 08032419752, ko 08123821575, 09029292926.

Continue Reading

Manyan Labarai

Hukumar Shari’a ta shirya kawo ƙarshen ƙwacen Waya a Kano

Published

on

Hukumar Shari’a ta jihar Kano, ta ce za ta tunkari matsalar ƙwacen Waya haɗin gwiwa da dukkan shugabannin kasuwannin wayoyi da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro da hukunci a jihar Kano, don kawo ƙarshen matsalar.

Kwamishina na biyu a hukumar Shari’a ta jihar Kano, Sheikh Ali Ɗan Abba, ne ya bayyana hakan a shafin sa na sada zumunta a ranar Asabar, biyo bayan yadda ake ci gaba da fuskantar ƙalubalen ƙwacen waya a birnin Kano, lamarin da ke sanadiyyar rayukan jama’a daga masu ƙwacen wayar, tare da asarar dukiyoyi.

Sheikh Ali Ɗan Abba, ya kuma ce, a makon da za a shiga ne Hukumar shari’a ta jihar Kano, za ta bayyana irin tsauraran matakan da za ta ɗauka a kan wannan masifar da ta gallabi al’ummar jihar, wato matsalar fashin Waya da Makami.

Tashar Dala FM Kano, ta ruwaito cewa, Sheikh Ɗan Abba, ya kuma yi addu’a akan lamarin, inda ya ce “Allah ya taimake mu ya kawo mana ƙarshen wannan masifar ta fashin Waya da makami a Kano”.

Wannan dai na zuwa ne yayin da al’ummar Kano, da masana harkokin tsaro, ke ci gaba da kiraye-kiraye ga mahukunta da su ƙara tashi tsaye wajen yin abinda ya dace don kawo ƙarshen ƙwacen waya, da faɗan Daba, da kuma shaye-shayen kayan maye, a jihar, la’akari da yadda lamarin ya ke damun jama’a.

Continue Reading

Trending